26) Sūrat Ash-Shu`arā'

Printed format

26) سُورَة الشُعَرَاء

Ţā-Sīn-Mīm َ026-001 ¦. S̃. M̃. طَا-سِين-مِيم
Tilka 'Āyātu Al-Kitābi Al-Mubīni َ026-002 Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne. تِلْكَ آيَاتُ الْكِتَابِ الْمُبِينِ
La`allaka Bākhi`un Nafsaka 'Allā Yakūnū Mu'uminīna َ026-003 Tsammãninka kai mai halakar da ranka ne, dõmin ba su kasance mũminai ba! لَعَلَّكَ بَاخِع ٌ نَفْسَكَ أَلاَّ يَكُونُوا مُؤْمِنِينَ
'In Nasha' Nunazzil `Alayhim Mina As-Samā'i 'Āyatan Fažallat 'A`nāquhum Lahā Khāđi`īna َ026-004 Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai. إِنْ نَشَأْ نُنَزِّلْ عَلَيْهِمْ مِنَ السَّمَاءِ آيَة ً فَظَلَّتْ أَعْنَاقُهُمْ لَهَا خَاضِعِينَ
Wa Mā Ya'tīhim Min Dhikrin Mina Ar-Raĥmāni Muĥdathin 'Illā Kānū `Anhu Mu`rīna َ026-005 Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa. وَمَا يَأْتِيهِمْ مِنْ ذِكْر ٍ مِنَ الرَّحْمَنِ مُحْدَث ٍ إِلاَّ كَانُوا عَنْهُ مُعْرِضِينَ
Faqad Kadhdhabū Fasaya'tīhim 'Anbā'u Mā Kānū Bihi Yastahzi'ūn َ026-006 To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu. فَقَدْ كَذَّبُوا فَسَيَأْتِيهِمْ أَنْبَاءُ مَا كَانُوا بِه ِِ يَسْتَهْزِئُون
'Awalam Yaraw 'Ilá Al-'Arđi Kam 'Anbatnā Fīhā Min Kulli Zawjin Karīmin َ026-007 Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau? أَوَلَمْ يَرَوْا إِلَى الأَرْضِ كَمْ أَنْبَتْنَا فِيهَا مِنْ كُلِّ زَوْج ٍ كَرِيم ٍ
'Inna Fī Dhālika La'āyatan  ۖ  Wa Mā Kāna 'Aktharuhum Mu'uminīna َ026-008 Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba. إِنَّ فِي ذَلِكَ لَآيَة ً  ۖ  وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُمْ مُؤْمِنِينَ
Wa 'Inna Rabbaka Lahuwa Al-`Azīzu Ar-Raĥīmu َ026-009 Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama. وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Wa 'Idh Nādá Rabbuka Mūsá 'Ani A'ti Al-Qawma Až-Žālimīna َ026-010 Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai. وَإِذْ نَادَى رَبُّكَ مُوسَى أَنِ ائْتِ الْقَوْمَ الظَّالِمِينَ
Qawma Fir`awna  ۚ  'Alā Yattaqūna َ026-011 "Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?" قَوْمَ فِرْعَوْنَ  ۚ  أَلاَ يَتَّقُونَ
Qāla Rabbi 'Innī 'Akhāfu 'An Yukadhdhibūni َ026-012 Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni. قَالَ رَبِّ إِنِّي أَخَافُ أَنْ يُكَذِّبُونِ
Wa Yađīqu Şadrī Wa Lā Yanţaliqu Lisānī Fa'arsil 'Ilá Hārūna َ026-013 "Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna. وَيَضِيقُ صَدْرِي وَلاَ يَنْطَلِقُ لِسَانِي فَأَرْسِلْ إِلَى هَارُونَ
Wa Lahum `Alayya Dhanbun Fa'akhāfu 'An Yaqtulūni َ026-014 "Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni." وَلَهُمْ عَلَيَّ ذَنْب ٌ فَأَخَافُ أَنْ يَقْتُلُونِ
Qāla Kallā  ۖ  Fādh/habā Bi'āyātinā  ۖ  'Innā Ma`akum Mustami`ūna َ026-015 Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre." قَالَ كَلاَّ  ۖ  فَاذْهَبَا بِآيَاتِنَا  ۖ  إِنَّا مَعَكُمْ مُسْتَمِعُونَ
Fa'tiyā Fir`awna Faqūlā 'Innā Rasūlu Rabbi Al-`Ālamīna َ026-016 "Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne." فَأْتِيَا فِرْعَوْنَ فَقُولاَ إِنَّا رَسُولُ رَبِّ الْعَالَمِينَ
'An 'Arsil Ma`anā Banī 'Isrā'īla َ026-017 "Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu." أَنْ أَرْسِلْ مَعَنَا بَنِي إِسْرَائِيلَ
Qāla 'Alam Nurabbika Fīnā Walīdāan Wa Labithta Fīnā Min `Umurika Sinīna َ026-018 Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?" قَالَ أَلَمْ نُرَبِّكَ فِينَا وَلِيدا ً وَلَبِثْتَ فِينَا مِنْ عُمُرِكَ سِنِينَ
Wa Fa`alta Fa`lataka Allatī Fa`alta Wa 'Anta Mina Al-Kāfirīna َ026-019 "Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?" وَفَعَلْتَ فَعْلَتَكَ الَّتِي فَعَلْتَ وَأَنْتَ مِنَ الْكَافِرِينَ
Qāla Fa`altuhā 'Idhāan Wa 'Anā Mina Ađ-Đāllīn َ026-020 Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin hushi." قَالَ فَعَلْتُهَا إِذا ً وَأَنَا مِنَ الضَّالِّين
Fafarartu Minkum Lammā Khiftukum Fawahaba Lī Rabbī Ĥukmāan Wa Ja`alanī Mina Al-Mursalīna َ026-021 "Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni." فَفَرَرْتُ مِنْكُمْ لَمَّا خِفْتُكُمْ فَوَهَبَ لِي رَبِّي حُكْما ً وَجَعَلَنِي مِنَ الْمُرْسَلِينَ
Wa Tilka Ni`matun Tamunnuhā `Alayya 'An `Abbadta Banī 'Isrā'īla َ026-022 "Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla." وَتِلْكَ نِعْمَة ٌ تَمُنُّهَا عَلَيَّ أَنْ عَبَّدْتَ بَنِي إِسْرَائِيلَ
Qāla Fir`awnu Wa Mā Rabbu Al-`Ālamīna َ026-023 Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?" قَالَ فِرْعَوْنُ وَمَا رَبُّ الْعَالَمِينَ
Qāla Rabbu As-Samāwāti Wa Al-'Arđi Wa Mā Baynahumā  ۖ  'In Kuntum Mūqinīna َ026-024 Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni." قَالَ رَبُّ السَّمَاوَاتِ وَالأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا  ۖ  إنْ كُنتُمْ مُوقِنِينَ
Qāla Liman Ĥawlahu 'Alā Tastami`ūna َ026-025 Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?" قَالَ لِمَنْ حَوْلَهُ~ُ أَلاَ تَسْتَمِعُونَ
Qāla Rabbukum Wa Rabbu 'Ābā'ikumu Al-'Awwalīna َ026-026 Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko." قَالَ رَبُّكُمْ وَرَبُّ آبَائِكُمُ الأَوَّلِينَ
Qāla 'Inna Rasūlakumu Al-Ladhī 'Ursila 'Ilaykum Lamajnūnun َ026-027 Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne." قَالَ إِنَّ رَسُولَكُمُ الَّذِي أُرْسِلَ إِلَيْكُمْ لَمَجْنُون ٌ
Qāla Rabbu Al-Mashriqi Wa Al-Maghribi Wa Mā Baynahumā  ۖ  'In Kuntum Ta`qilūna َ026-028 Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta." قَالَ رَبُّ الْمَشْرِقِ وَالْمَغْرِبِ وَمَا بَيْنَهُمَا  ۖ  إِنْ كُنْتُمْ تَعْقِلُونَ
Qāla La'ini Attakhadhta 'Ilahāan Ghayrī La'aj`alannaka Mina Al-Masjūnīna َ026-029 Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru." قَالَ لَئِنِ اتَّخَذْتَ إِلَهَاً غَيْرِي لَأَجْعَلَنَّكَ مِنَ الْمَسْجُونِينَ
Qāla 'Awalaw Ji'tuka Bishay'in Mubīnin َ026-030 Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?" قَالَ أَوَلَوْ جِئْتُكَ بِشَيْء ٍ مُبِين ٍ
Qāla Fa'ti Bihi 'In Kunta Mina Aş-Şādiqīna َ026-031 Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya." قَالَ فَأْتِ بِهِ~ِ إِنْ كُنْتَ مِنَ الصَّادِقِينَ
Fa'alqá `Aşāhu Fa'idhā Hiya Thu`bānun Mubīnun َ026-032 Sai ya jẽfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne. فَأَلْقَى عَصَاه ُُ فَإِذَا هِيَ ثُعْبَان ٌ مُبِين ٌ
Wa Naza`a Yadahu Fa'idhā Hiya Bayđā'u Lilnnāžirīna َ026-033 Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo. وَنَزَعَ يَدَه ُُ فَإِذَا هِيَ بَيْضَاءُ لِلنَّاظِرِينَ
Qāla Lilmala'i Ĥawlahu 'Inna Hādhā Lasāĥirun `Alīmun َ026-034 (Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi! قَالَ لِلْمَلَإِ حَوْلَهُ~ُ إِنَّ هَذَا لَسَاحِرٌ عَلِيم ٌ
Yurīdu 'An Yukhrijakum Min 'Arđikum Bisiĥrihi Famādhā Ta'murūna َ026-035 "Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mẽne ne kuke shãwartãwa?" يُرِيدُ أَنْ يُخْرِجَكُمْ مِنْ أَرْضِكُمْ بِسِحْرِه ِِ فَمَاذَا تَأْمُرُونَ
Qālū 'Arjihi Wa 'Akhāhu Wa Ab`ath Al-Madā'ini Ĥāshirīna َ026-036 Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne." قَالُوا أَرْجِه ِِ وَأَخَاه ُُ وَابْعَثْ فِي الْمَدَائِنِ حَاشِرِينَ
Ya'tūka Bikulli Saĥĥārin `Alīmin َ026-037 "Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani." يَأْتُوكَ بِكُلِّ سَحَّارٍ عَلِيم ٍ
Fajumi`a As-Saĥaratu Limīqāti Yawmin Ma`lūmin َ026-038 Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne. فَجُمِعَ السَّحَرَةُ لِمِيقَاتِ يَوْم ٍ مَعْلُوم ٍ
Wa Qīla Lilnnāsi Hal 'Antum Mujtami`ūna َ026-039 Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne? وَقِيلَ لِلنَّاسِ هَلْ أَنْتُمْ مُجْتَمِعُونَ
La`allanā Nattabi`u As-Saĥarata 'In Kānū Humu Al-Ghālibīna َ026-040 "Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya." لَعَلَّنَا نَتَّبِعُ السَّحَرَةَ إِنْ كَانُوا هُمُ الْغَالِبِينَ
Falammā Jā'a As-Saĥaratu Qālū Lifir`awna 'A'inna Lanā La'ajrāan 'In Kunnā Naĥnu Al-Ghālibīna َ026-041 To, a lõkacin da masihirta suka jẽ suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?" فَلَمَّا جَاءَ السَّحَرَةُ قَالُوا لِفِرْعَوْنَ أَئِنَّ لَنَا لَأَجْرا ً إِنْ كُنَّا نَحْنُ الْغَالِبِينَ
Qāla Na`am Wa 'Innakum 'Idhāan Lamina Al-Muqarrabīna َ026-042 Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai." قَالَ نَعَمْ وَإِنَّكُمْ إِذا ً لَمِنَ الْمُقَرَّبِينَ
Qāla Lahum Mūsá 'Alqū Mā 'Antum Mulqūna َ026-043 Mũsã ya ce musu, "Ku jẽfa abin da kuke mãsu jẽfãwa." قَالَ لَهُمْ مُوسَى أَلْقُوا مَا أَنْتُمْ مُلْقُونَ
Fa'alqaw Ĥibālahum Wa `Işīyahum Wa Qālū Bi`izzati Fir`awna 'Innā Lanaĥnu Al-Ghālibūna َ026-044 Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya." فَأَلْقَوْا حِبَالَهُمْ وَعِصِيَّهُمْ وَقَالُوا بِعِزَّةِ فِرْعَوْنَ إِنَّا لَنَحْنُ الْغَالِبُونَ
Fa'alqá Mūsá `Aşāhu Fa'idhā Hiya Talqafu Mā Ya'fikūna َ026-045 Sai Mũsa ya jẽfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya. فَأَلْقَى مُوسَى عَصَاه ُُ فَإِذَا هِيَ تَلْقَفُ مَا يَأْفِكُونَ
Fa'ulqiya As-Saĥaratu Sājidīna َ026-046 Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada. فَأُلْقِيَ السَّحَرَةُ سَاجِدِينَ
Qālū 'Āmannā Birabbi Al-`Ālamīna َ026-047 Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta." قَالُوا آمَنَّا بِرَبِّ الْعَالَمِينَ
Rabbi Mūsá Wa Hārūna َ026-048 "Ubangijin Mũsa da Hãrũna." رَبِّ مُوسَى وَهَارُونَ
Qāla 'Āmantum Lahu Qabla 'An 'Ādhana Lakum  ۖ  'Innahu Lakabīrukumu Al-Ladhī `Allamakumu As-Siĥra Falasawfa Ta`lamūna  ۚ  La'uqaţţi`anna 'Aydiyakum Wa 'Arjulakum Min Khilāfin Wa La'uşallibannakum 'Ajma`īna َ026-049 Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa,zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya." قَالَ آمَنْتُمْ لَه ُُ قَبْلَ أَنْ آذَنَ لَكُمْ  ۖ  إِنَّه ُُ لَكَبِيرُكُمُ الَّذِي عَلَّمَكُمُ السِّحْرَ فَلَسَوْفَ تَعْلَمُونَ  ۚ  لَأُقَطِّعَنَّ أَيْدِيَكُمْ وَأَرْجُلَكُمْ مِنْ خِلاَف ٍ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمْ أَجْمَعِينَ
Qālū Lā Đayra  ۖ  'Innā 'Ilá Rabbinā Munqalibūna َ026-050 Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu." قَالُوا لاَ ضَيْرَ  ۖ  إِنَّا إِلَى رَبِّنَا مُنْقَلِبُونَ
'Innā Naţma`u 'An Yaghfira Lanā Rabbunā Khaţāyānā 'An Kunnā 'Awwala Al-Mu'uminīna َ026-051 "Lalle ne mu munã kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gãfarta mana kurakuranmu dõmin mun kasance farkon mãsu ĩmãni." إِنَّا نَطْمَعُ أَنْ يَغْفِرَ لَنَا رَبُّنَا خَطَايَانَا أَنْ كُنَّا أَوَّلَ الْمُؤْمِنِينَ
Wa 'Awĥaynā 'Ilá Mūsá 'An 'Asri Bi`ibādī 'Innakum Muttaba`ūna َ026-052 Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cẽwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã ne. وَأَوْحَيْنَا إِلَى مُوسَى أَنْ أَسْرِ بِعِبَادِي إِنَّكُمْ مُتَّبَعُونَ
Fa'arsala Fir`awnu Fī Al-Madā'ini Ĥāshirīna َ026-053 Sai Fir'auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne. فَأَرْسَلَ فِرْعَوْنُ فِي الْمَدَائِنِ حَاشِرِينَ
'Inna Hā'uulā' Lashirdhimatun Qalīlūna َ026-054 "Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan." إِنَّ هَاؤُلاَء لَشِرْذِمَة ٌ قَلِيلُونَ
Wa 'Innahum Lanā Laghā'ižūna َ026-055 "Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne." وَإِنَّهُمْ لَنَا لَغَائِظُونَ
Wa 'Innā Lajamī`un Ĥādhirūna َ026-056 "Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne." وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَاذِرُونَ
Fa'akhrajnāhum Min Jannātin Wa `Uyūnin َ026-057 Sai Muka fitar da su daga gonaki da marẽmari. فَأَخْرَجْنَاهُمْ مِنْ جَنَّات ٍ وَعُيُون ٍ
Wa Kunūzin Wa Maqāmin Karīmin َ026-058 Da taskõki da mazauni mai kyau. وَكُنُوز ٍ وَمَقَام ٍ كَرِيم ٍ
Kadhālika Wa 'Awrathnāhā Banī 'Isrā'īla َ026-059 Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla. كَذَلِكَ وَأَوْرَثْنَاهَا بَنِي إِسْرَائِيلَ
Fa'atba`ūhum Mushriqīna َ026-060 Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã. فَأَتْبَعُوهُمْ مُشْرِقِينَ
Falammā Tarā'á Al-Jam`āni Qāla 'Aşĥābu Mūsá 'Innā Lamudrakūna َ026-061 Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne." فَلَمَّا تَرَاءَى الْجَمْعَانِ قَالَ أَصْحَابُ مُوسَى إِنَّا لَمُدْرَكُونَ
Qāla Kallā  ۖ  'Inna Ma`iya Rabbī Sayahdīni َ026-062 Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni." قَالَ كَلاَّ  ۖ  إِنَّ مَعِيَ رَبِّي سَيَهْدِينِ
Fa'awĥaynā 'Ilá Mūsá 'Ani Ađrib Bi`aşāka Al-Baĥra  ۖ  Fānfalaqa Fakāna Kullu Firqin Kālţţawdi Al-`Ažīmi َ026-063 Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge, kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma. فَأَوْحَيْنَا إِلَى مُوسَى أَنِ اضْرِبْ بِعَصَاكَ الْبَحْرَ  ۖ  فَانفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرْق ٍ كَالطَّوْدِ الْعَظِيمِ
Wa 'Azlafnā Thamma Al-'Ākharīna َ026-064 Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can. وَأَزْلَفْنَا ثَمَّ الآخَرِينَ
Wa 'Anjaynā Mūsá Wa Man Ma`ahu 'Ajma`īna َ026-065 Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya. وَأَنْجَيْنَا مُوسَى وَمَنْ مَعَهُ~ُ أَجْمَعِينَ
Thumma 'Aghraq Al-'Ākharīna َ026-066 Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen. ثُمَّ أَغْرَقْنَا الآخَرِينَ
'Inna Fī Dhālika La'āyatan  ۖ  Wa Mā Kāna 'Aktharuhum Mu'uminīna َ026-067 Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba. إِنَّ فِي ذَلِكَ لَآيَة ً  ۖ  وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُمْ مُؤْمِنِينَ
Wa 'Inna Rabbaka Lahuwa Al-`Azīzu Ar-Raĥīmu َ026-068 Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai. وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Wa Atlu `Alayhim Naba'a 'Ibrāhīma َ026-069 Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm. وَاتْلُ عَلَيْهِمْ نَبَأَ إِبْرَاهِيمَ
'Idh Qāla Li'abīhi Wa Qawmihi Mā Ta`budūna َ026-070 A sã'ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bauta wa?" إِذْ قَالَ لِأَبِيه ِِ وَقَوْمِه ِِ مَا تَعْبُدُونَ
Qālū Na`budu 'Aşnāmāan Fanažallu Lahā `Ākifīna َ026-071 Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su." قَالُوا نَعْبُدُ أَصْنَاما ً فَنَظَلُّ لَهَا عَاكِفِينَ
Qāla Hal Yasma`ūnakum 'Idh Tad`ūna َ026-072 Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?" قَالَ هَلْ يَسْمَعُونَكُمْ إِذْ تَدْعُونَ
'Aw Yanfa`ūnakum 'Aw Yađurrūna َ026-073 "Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?" أَوْ يَنْفَعُونَكُمْ أَوْ يَضُرُّونَ
Qālū Bal Wajadnā 'Ābā'anā Kadhālika Yaf`alūna َ026-074 Suka ce: "Ã'a mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa." قَالُوا بَلْ وَجَدْنَا آبَاءَنَا كَذَلِكَ يَفْعَلُونَ
Qāla 'Afara'aytum Mā Kuntum Ta`budūna َ026-075 Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?" قَالَ أَفَرَأَيْتُمْ مَا كُنْتُمْ تَعْبُدُونَ
'Antum Wa 'Ābā'uukumu Al-'Aqdamūna َ026-076 "Kũ da ubanninku mafi daɗẽwa?" أَنْتُمْ وَآبَاؤُكُمُ الأَقْدَمُونَ
Fa'innahum `Adūwun Lī 'Illā Rabba Al-`Ālamīna َ026-077 "To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu." فَإِنَّهُمْ عَدُوّ ٌ لِي إِلاَّ رَبَّ الْعَالَمِينَ
Al-Ladhī Khalaqanī Fahuwa Yahdīni َ026-078 "Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni." الَّذِي خَلَقَنِي فَهُوَ يَهْدِينِ
Wa Al-Ladhī Huwa Yuţ`imunī Wa Yasqīni َ026-079 "Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni." وَالَّذِي هُوَ يُطْعِمُنِي وَيَسْقِينِ
Wa 'Idhā Mariđtu Fahuwa Yashfīni َ026-080 "Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni." وَإِذَا مَرِضْتُ فَهُوَ يَشْفِينِ
Wa Al-Ladhī Yumītunī Thumma Yuĥyīni َ026-081 "Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni." وَالَّذِي يُمِيتُنِي ثُمَّ يُحْيِينِ
Wa Al-Ladhī 'Aţma`u 'An Yaghfira Lī Khī'atī Yawma Ad-Dīni َ026-082 "Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako." وَالَّذِي أَطْمَعُ أَنْ يَغْفِرَ لِي خَطِيئَتِي يَوْمَ الدِّينِ
Rabbi Hab Lī Ĥukmāan Wa 'Alĥiqnī Biş-Şāliĥīna َ026-083 "Ya Ubangijĩna! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai." رَبِّ هَبْ لِي حُكْما ً وَأَلْحِقْنِي بِالصَّالِحِينَ
Wa Aj`al Lī Lisāna Şidqin Al-'Ākhirīna َ026-084 "Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya a cikin mutãnen ƙarshe." وَاجْعَلْ لِي لِسَانَ صِدْق ٍ فِي الآخِرِينَ
Wa Aj`alnī Min Warathati Jannati An-Na`īmi َ026-085 "Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima." وَاجْعَلْنِي مِنْ وَرَثَةِ جَنَّةِ النَّعِيمِ
Wa Aghfir Li'abī 'Innahu Kāna Mina Ađ-Đāllīna َ026-086 "Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu." وَاغْفِرْ لِأَبِي إِنَّه ُُ كَانَ مِنَ الضَّالِّينَ
Wa Lā Tukhzinī Yawma Yub`athūna َ026-087 "Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su." وَلاَ تُخْزِنِي يَوْمَ يُبْعَثُونَ
Yawma Lā Yanfa`u Mālun Wa Lā Banūna َ026-088 "A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi." يَوْمَ لاَ يَنْفَعُ مَال ٌ وَلاَ بَنُونَ
'Illā Man 'Atá Al-Laha Biqalbin Salīmin َ026-089 "Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki." إِلاَّ مَنْ أَتَى اللَّهَ بِقَلْب ٍ سَلِيم ٍ
Wa 'Uzlifati Al-Jannatu Lilmuttaqīna َ026-090 Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa. وَأُزْلِفَتِ الْجَنَّةُ لِلْمُتَّقِينَ
Wa Burrizati Al-Jaĥīmu Lilghāwīna َ026-091 Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku. وَبُرِّزَتِ الْجَحِيمُ لِلْغَاوِينَ
Wa Qīla Lahum 'Ayna Mā Kuntum Ta`budūna َ026-092 Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?" وَقِيلَ لَهُمْ أَيْنَ مَا كُنْتُمْ تَعْبُدُونَ
Min Dūni Al-Lahi Hal Yanşurūnakum 'Aw Yantaşirūna َ026-093 "Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?" مِنْ دُونِ اللَّهِ هَلْ يَنْصُرُونَكُمْ أَوْ يَنْتَصِرُونَ
Fakubkibū Fīhā Hum Wa Al-Ghāwūna َ026-094 Sai aka kikkife su a cikinta, su da halakakkun. فَكُبْكِبُوا فِيهَا هُمْ وَالْغَاوُونَ
Wa Junūdu 'Iblīsa 'Ajma`ūna َ026-095 Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya. وَجُنُودُ إِبْلِيسَ أَجْمَعُونَ
Qālū Wa Hum Fīhā Yakhtaşimūna َ026-096 Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma, قَالُوا وَهُمْ فِيهَا يَخْتَصِمُونَ
Ta-Allāhi 'In Kunnā Lafī Đalālin Mubīnin َ026-097 "Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna." تَاللَّهِ إِنْ كُنَّا لَفِي ضَلاَل ٍ مُبِين ٍ
'Idh Nusawwīkum Birabbi Al-`Ālamīna َ026-098 "A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu. إِذْ نُسَوِّيكُمْ بِرَبِّ الْعَالَمِينَ
Wa Mā 'Ađallanā 'Illā Al-Mujrimūna َ026-099 "Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi." وَمَا أَضَلَّنَا إِلاَّ الْمُجْرِمُونَ
Famā Lanā Min Shāfi`īna َ026-100 "Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta." فَمَا لَنَا مِنْ شَافِعِينَ
Wa Lā Şadīqin Ĥamīmin َ026-101 "Kuma bã mu da abõki, masõyi." وَلاَ صَدِيقٍ حَمِيم ٍ
Falaw 'Anna Lanā Karratan Fanakūna Mina Al-Mu'uminīna َ026-102 "Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!" فَلَوْ أَنَّ لَنَا كَرَّة ً فَنَكُونَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ
'Inna Fī Dhālika La'āyatan  ۖ  Wa Mā Kāna 'Aktharuhum Mu'uminīna َ026-103 Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba. إِنَّ فِي ذَلِكَ لَآيَة ً  ۖ  وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُمْ مُؤْمِنِينَ
Wa 'Inna Rabbaka Lahuwa Al-`Azīzu Ar-Raĥīmu َ026-104 Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai. وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Kadhdhabat Qawmu Nūĥin Al-Mursalīna َ026-105 Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni. كَذَّبَتْ قَوْمُ نُوح ٍ الْمُرْسَلِينَ
'Idh Qāla Lahum 'Akhūhum Nūĥun 'Alā Tattaqūna َ026-106 A lõkacin da ɗan'uwansu, Nũhu, ya ce musu, "Shin, bã zã ku yi taƙawa ba?" إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ نُوحٌ أَلاَ تَتَّقُونَ
'Innī Lakum Rasūlun 'Amīnun َ026-107 "Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce." إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِين ٌ
Fāttaqū Al-Laha Wa 'Aţī`ūni َ026-108 "To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã." فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ
Wa Mā 'As'alukum `Alayhi Min 'Ajrin  ۖ  'In 'Ajrī 'Illā `Alá Rabbi Al-`Ālamīna َ026-109 "Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu." وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْر ٍ  ۖ  إِنْ أَجْرِي إِلاَّ عَلَى رَبِّ الْعَالَمِينَ
Fāttaqū Al-Laha Wa 'Aţī`ūni َ026-110 "Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã." فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ
Qālū 'Anu'uminu Laka Wa Attaba`aka Al-'Ardhalūna َ026-111 Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?" قَالُوا أَنُؤْمِنُ لَكَ وَاتَّبَعَكَ الأَرْذَلُونَ
Qāla Wa Mā `Ilmī Bimā Kānū Ya`malūna َ026-112 Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa." قَالَ وَمَا عِلْمِي بِمَا كَانُوا يَعْمَلُونَ
'In Ĥisābuhum 'Illā `Alá Rabbī  ۖ  Law Tash`urūna َ026-113 "Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancẽwa." إِنْ حِسَابُهُمْ إِلاَّ عَلَى رَبِّي  ۖ  لَوْ تَشْعُرُونَ
Wa Mā 'Anā Biţāridi Al-Mu'uminīna َ026-114 "Ban zama mai kõre mũminai ba." وَمَا أَنَا بِطَارِدِ الْمُؤْمِنِينَ
'In 'Anā 'Illā Nadhīrun Mubīnun َ026-115 "Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa." إِنْ أَنَا إِلاَّ نَذِير ٌ مُبِين ٌ
Qālū La'in Lam Tantahi Yā Nūĥu Latakūnanna Mina Al-Marjūmīna َ026-116 Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa" قَالُوا لَئِنْ لَمْ تَنْتَه ِِ يَانُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ الْمَرْجُومِينَ
Qāla Rabbi 'Inna Qawmī Kadhdhabūni َ026-117 Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni." قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوْمِي كَذَّبُونِ
Fāftaĥ Baynī Wa Baynahum Fatĥāan Wa Najjinī Wa Man Ma`ī Mina Al-Mu'uminīna َ026-118 "Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai." فَافْتَحْ بَيْنِي وَبَيْنَهُمْ فَتْحا ً وَنَجِّنِي وَمَنْ مَعِي مِنَ الْمُؤْمِنِينَ
Fa'anjaynāhu Wa Man Ma`ahu Fī Al-Fulki Al-Mashĥūni َ026-119 Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi. فَأَنجَيْنَاه ُُ وَمَنْ مَعَه ُُ فِي الْفُلْكِ الْمَشْحُونِ
Thumma 'Aghraqnā Ba`du Al-Bāqīna َ026-120 Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran. ثُمَّ أَغْرَقْنَا بَعْدُ الْبَاقِينَ
'Inna Fī Dhālika La'āyatan  ۖ  Wa Mā Kāna 'Aktharuhum Mu'uminīna َ026-121 Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba. إِنَّ فِي ذَلِكَ لَآيَة ً  ۖ  وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُمْ مُؤْمِنِينَ
Wa 'Inna Rabbaka Lahuwa Al-`Azīzu Ar-Raĥīmu َ026-122 Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama. وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Kadhdhabat `Ādun Al-Mursalīna َ026-123 Ãdãwa sun ƙaryata Manzanni. كَذَّبَتْ عَاد ٌ الْمُرْسَلِينَ
'Idh Qāla Lahum 'Akhūhum Hūdun 'Alā Tattaqūna َ026-124 A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?" إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ هُودٌ أَلاَ تَتَّقُونَ
'Innī Lakum Rasūlun 'Amīnun َ026-125 "Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce." إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِين ٌ
Fāttaqū Al-Laha Wa 'Aţī`ūni َ026-126 "Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã." فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ
Wa Mā 'As'alukum `Alayhi Min 'Ajrin  ۖ  'In 'Ajrī 'Illā `Alá Rabbi Al-`Ālamīna َ026-127 "Kuma bã ni tambayar wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba, fãce daga Ubangijin halittu." وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْر ٍ  ۖ  إِنْ أَجْرِي إِلاَّ عَلَى رَبِّ الْعَالَمِينَ
'Atabnūna Bikulli Rī`in 'Āyatan Ta`bathūna َ026-128 "Shin, kunã yin ginin sitadiyo a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?" أَتَبْنُونَ بِكُلِّ رِيع ٍ آيَة ً تَعْبَثُونَ
Wa Tattakhidhūna Maşāni`a La`allakum Takhludūna َ026-129 "Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?" وَتَتَّخِذُونَ مَصَانِعَ لَعَلَّكُمْ تَخْلُدُونَ
Wa 'Idhā Baţashtum Baţashtum Jabbārīna َ026-130 "Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa." وَإِذَا بَطَشْتُمْ بَطَشْتُمْ جَبَّارِينَ
Fāttaqū Al-Laha Wa 'Aţī`ūni َ026-131 "To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã." فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ
Wa Attaqū Al-Ladhī 'Amaddakum Bimā Ta`lamūna َ026-132 "Ku ji tsõron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani." وَاتَّقُوا الَّذِي أَمَدَّكُمْ بِمَا تَعْلَمُونَ
'Amaddakum Bi'an`āmin Wa Banīna َ026-133 "Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya." أَمَدَّكُمْ بِأَنْعَام ٍ وَبَنِينَ
Wa Jannātin Wa `Uyūnin َ026-134 "Da gõnaki da marẽmari." وَجَنَّات ٍ وَعُيُون ٍ
'Innī 'Akhāfu `Alaykum `Adhāba Yawmin `Ažīmin َ026-135 "Lalle ne nĩ, inã ji muku tsõron azãbar wani yini mai girma." إِنِّي أَخَافُ عَلَيْكُمْ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيم ٍ
Qālū Sawā'un `Alaynā 'Awa`ažta 'Am Lam Takun Mina Al-Wā`ižīna َ026-136 Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Kã yi wa'azi kõ ba ka kasance daga mãsu wa'azi ba." قَالُوا سَوَاءٌ عَلَيْنَا أَوَعَظْتَ أَمْ لَمْ تَكُنْ مِنَ الْوَاعِظِينَ
'In Hādhā 'Illā Khuluqu Al-'Awwalīna َ026-137 "Wannan abu bai zamõ ba fãce hãlãyen mutãnen farko." إِنْ هَذَا إِلاَّ خُلُقُ الأَوَّلِينَ
Wa Mā Naĥnu Bimu`adhdhabīna َ026-138 "Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba." وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ
Fakadhdhabūhu Fa'ahlaknāhum  ۗ  'Inna Fī Dhālika La'āyatan  ۖ  Wa Mā Kāna 'Aktharuhum Mu'uminīna َ026-139 Sabõda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da sũ.Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba. فَكَذَّبُوه ُُ فَأَهْلَكْنَاهُمْ  ۗ  إِنَّ فِي ذَلِكَ لَآيَة ً  ۖ  وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُمْ مُؤْمِنِينَ
Wa 'Inna Rabbaka Lahuwa Al-`Azīzu Ar-Raĥīmu َ026-140 Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai. وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Kadhdhabat Thamūdu Al-Mursalīna َ026-141 Samũdãwa sun ƙaryata Manzanni. كَذَّبَتْ ثَمُودُ الْمُرْسَلِينَ
'Idh Qāla Lahum 'Akhūhum Şāliĥun 'Alā Tattaqūna َ026-142 A lõkacin da ɗan'uwansu Sãlihu ya ce: "Shin, bã zã ku bi Allah da taƙawa ba?" إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ صَالِحٌ أَلاَ تَتَّقُونَ
'Innī Lakum Rasūlun 'Amīnun َ026-143 "Lalle ne nĩ zuwã gare ku, Manzo ne, amintacce." إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِين ٌ
Fāttaqū Al-Laha Wa 'Aţī`ūni َ026-144 "Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã. فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ
Wa Mā 'As'alukum `Alayhi Min 'Ajrin  ۖ  'In 'Ajriya 'Illā `Alá Rabbi Al-`Ālamīna َ026-145 "Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba fãce da a Ubangijin halittu." وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْر ٍ  ۖ  إِنْ أَجْرِيَ إِلاَّ عَلَى رَبِّ الْعَالَمِينَ
'Atutrakūna Fī Mā Hāhunā 'Āminīna َ026-146 "Shin, anã barin ku a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?" أَتُتْرَكُونَ فِي مَا هَاهُنَا آمِنِينَ
Fī Jannātin Wa `Uyūnin َ026-147 "A cikin gõnaki da marẽmari." فِي جَنَّات ٍ وَعُيُون ٍ
Wa Zurū`in Wa Nakhlin Ţal`uhā Hađīmun َ026-148 "Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi mãsu narkẽwa a ciki?" وَزُرُوع ٍ وَنَخْل ٍ طَلْعُهَا هَضِيم ٌ
Wa Tanĥitūna Mina Al-Jibāli Buyūtāanrihīna َ026-149 "Kuma kunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, kunã mãsu alfãhari?" وَتَنْحِتُونَ مِنَ الْجِبَالِ بُيُوتا ً فَارِهِينَ
Fāttaqū Al-Laha Wa 'Aţī`ūni َ026-150 "Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã." فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ
Wa Lā Tuţī`ū 'Amra Al-Musrifīna َ026-151 "Kada ku yi ɗã'ã ga umurnin maɓarnata." وَلاَ تُطِيعُوا أَمْرَ الْمُسْرِفِينَ
Al-Ladhīna Yufsidūna Fī Al-'Arđi Wa Lā Yuşliĥūna َ026-152 "Waɗanda suke yin ɓarna a cikin ƙasa, kuma bã su kyautatãwa." الَّذِينَ يُفْسِدُونَ فِي الأَرْضِ وَلاَ يُصْلِحُونَ
Qālū 'Innamā 'Anta Mina Al-Musaĥĥarīna َ026-153 Suka ce: "Kai daga mãsu sihiri kurum kake." قَالُوا إِنَّمَا أَنْتَ مِنَ الْمُسَحَّرِينَ
Mā 'Anta 'Illā Basharun Mithlunā Fa'ti Bi'āyatin 'In Kunta Mina Aş-Şādiqīna َ026-154 "Bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu. To, kã zo da wata ãyã idan kã kasance daga mãsu gaskiya." مَا أَنْتَ إِلاَّ بَشَر ٌ مِثْلُنَا فَأْتِ بِآيَة ٍ إِنْ كُنْتَ مِنَ الصَّادِقِينَ
Qāla Hadhihi Nāqatun Lahā Shirbun Wa Lakum Shirbu Yawmin Ma`lūmin َ026-155 Ya ce: "Wannan rãkuma ce tanã da shan yini, kuma kunã da shan yini sasanne." قَالَ هَذِه ِِ نَاقَة ٌ لَهَا شِرْب ٌ وَلَكُمْ شِرْبُ يَوْم ٍ مَعْلُوم ٍ
Wa Lā Tamassūhā Bisū'in Faya'khudhakum `Adhābu Yawmin `Ažīmin َ026-156 "Kada ku shãfe ta da cũta har azãbar yini mai girmã ta shãfe ku." وَلاَ تَمَسُّوهَا بِسُوء ٍ فَيَأْخُذَكُمْ عَذَابُ يَوْمٍ عَظِيم ٍ
Fa`aqarūhā Fa'aşbaĥū Nādimīna َ026-157 Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma. فَعَقَرُوهَا فَأَصْبَحُوا نَادِمِينَ
Fa'akhadhahumu Al-`Adhābu  ۗ  'Inna Fī Dhālika La'āyatan  ۖ  Wa Mā Kāna 'Aktharuhum Mu'uminīna َ026-158 Sabõda haka azãba ta kãma su. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba. فَأَخَذَهُمُ الْعَذَابُ  ۗ  إِنَّ فِي ذَلِكَ لَآيَة ً  ۖ  وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُمْ مُؤْمِنِينَ
Wa 'Inna Rabbaka Lahuwa Al-`Azīzu Ar-Raĥīmu َ026-159 Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai. وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Kadhdhabat Qawmu Lūţin Al-Mursalīna َ026-160 Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata Manzanni. كَذَّبَتْ قَوْمُ لُوط ٍ الْمُرْسَلِينَ
'Idh Qāla Lahum 'Akhūhum Lūţun 'Alā Tattaqūna َ026-161 A lõkacin da ɗan'uwansu, Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?" إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ لُوطٌ أَلاَ تَتَّقُونَ
'Innī Lakum Rasūlun 'Amīnun َ026-162 "Lalle ne nĩ, zuwa gare ku, Manzõ ne, amintacce." إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِين ٌ
Fāttaqū Al-Laha Wa 'Aţī`ūni َ026-163 "Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã." فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ
Wa Mā 'As'alukum `Alayhi Min 'Ajrin  ۖ  'In 'Ajriya 'Illā `Alá Rabbi Al-`Ālamīna َ026-164 "Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra, Ijãrãta ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu." وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْر ٍ  ۖ  إِنْ أَجْرِيَ إِلاَّ عَلَى رَبِّ الْعَالَمِينَ
'Ata'tūna Adh-Dhukrāna Mina Al-`Ālamīna َ026-165 "Shin kunã jẽ wa maza daga cikin talikai?" أَتَأْتُونَ الذُّكْرَانَ مِنَ الْعَالَمِينَ
Wa Tadharūna Mā Khalaqa Lakum Rabbukum Min 'Azwājikum  ۚ  Bal 'Antum Qawmun `Ādūna َ026-166 "Kuma kunã barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga mãtanku? Ã'a, ku mutãne ne mãsu ƙẽtarẽwa!" وَتَذَرُونَ مَا خَلَقَ لَكُمْ رَبُّكُمْ مِنْ أَزْوَاجِكُمْ  ۚ  بَلْ أَنْتُمْ قَوْمٌ عَادُونَ
Qālū La'in Lam Tantahi Yā Lūţu Latakūnanna Mina Al-Mukhrajīna َ026-167 Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)." قَالُوا لَئِنْ لَمْ تَنْتَه ِِ يَا لُوطُ لَتَكُونَنَّ مِنَ الْمُخْرَجِينَ
Qāla 'Innī Li`amalikum Mina Al-Qālīna َ026-168 Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa." قَالَ إِنِّي لِعَمَلِكُمْ مِنَ الْقَالِينَ
Rabbi Najjinī Wa 'Ahlī Mimmā Ya`malūna َ026-169 "Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa." رَبِّ نَجِّنِي وَأَهْلِي مِمَّا يَعْمَلُونَ
Fanajjaynāhu Wa 'Ahlahu 'Ajma`īna َ026-170 Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya. فَنَجَّيْنَاه ُُ وَأَهْلَهُ~ُ أَجْمَعِينَ
'Illā `Ajūzāan Al-Ghābirīna َ026-171 Fãce wata tsõhuwa a cikin mãsu wanzuwa. إِلاَّ عَجُوزا ً فِي الْغَابِرِينَ
Thumma Dammarnā Al-'Ākharīna َ026-172 Sa'an nan kuma Muka darkãke wasu. ثُمَّ دَمَّرْنَا الآخَرِينَ
Wa 'Amţarnā `Alayhim Maţarāan  ۖ  Fasā'a Maţaru Al-Mundharīna َ026-173 Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana. وَأَمْطَرْنَا عَلَيْهِمْ مَطَرا ً  ۖ  فَسَاءَ مَطَرُ الْمُنذَرِينَ
'Inna Fī Dhālika La'āyatan  ۖ  Wa Mā Kāna 'Aktharuhum Mu'uminīna َ026-174 Lalle ne ga wannan, akwai ãyã, kuma mafi yawansu bã su kasance mãsu ĩmãni ba. إِنَّ فِي ذَلِكَ لَآيَة ً  ۖ  وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُمْ مُؤْمِنِينَ
Wa 'Inna Rabbaka Lahuwa Al-`Azīzu Ar-Raĥīmu َ026-175 Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai. وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Kadhdhaba 'Aşĥābu Al-'Aykati Al-Mursalīna َ026-176 Ma'abũta ƙunci sun ƙaryata Manzanni. كَذَّبَ أَصْحَابُ الأَيْكَةِ الْمُرْسَلِينَ
'Idh Qāla Lahum Shu`aybun 'Alā Tattaqūna َ026-177 A lõkacin da Shu'aibu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?" إِذْ قَالَ لَهُمْ شُعَيْبٌ أَلاَ تَتَّقُونَ
'Innī Lakum Rasūlun 'Amīnun َ026-178 "Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce." إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِين ٌ
Fāttaqū Al-Laha Wa 'Aţī`ūni َ026-179 "Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã." فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ
Wa Mā 'As'alukum `Alayhi Min 'Ajrin  ۖ  'In 'Ajriya 'Illā `Alá Rabbi Al-`Ālamīna َ026-180 "Kuma ba ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu." وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْر ٍ  ۖ  إِنْ أَجْرِيَ إِلاَّ عَلَى رَبِّ الْعَالَمِينَ
'Awfū Al-Kayla Wa Lā Takūnū Mina Al-Mukhsirīna َ026-181 "Ku cika mũdu, kuma kada ku kasance daga mãsu sanyãwar hasãra (ga mutãne)." أَوْفُوا الْكَيْلَ وَلاَ تَكُونُوا مِنَ الْمُخْسِرِينَ
Wa Zinū Bil-Qisţāsi Al-Mustaqīmi َ026-182 "Kuma ku yi awo da sikẽli daidaitacce." وَزِنُوا بِالْقِسْطَاسِ الْمُسْتَقِيمِ
Wa Lā Tabkhasū An-Nāsa 'Ashyā'ahum Wa Lā Ta`thaw Fī Al-'Arđi Mufsidīna َ026-183 "Kuma kada ku nakasa wa mutãne abũbuwansu kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa kuna mãsu ɓarna." وَلاَ تَبْخَسُوا النَّاسَ أَشْيَاءَهُمْ وَلاَ تَعْثَوْا فِي الأَرْضِ مُفْسِدِينَ
Wa Attaqū Al-Ladhī Khalaqakum Wa Al-Jibillata Al-'Awwalīna َ026-184 "Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko." وَاتَّقُوا الَّذِي خَلَقَكُمْ وَالْجِبِلَّةَ الأَوَّلِينَ
Qālū 'Innamā 'Anta Mina Al-Musaĥĥarīna َ026-185 Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne." قَالُوا إِنَّمَا أَنْتَ مِنَ الْمُسَحَّرِينَ
Wa Mā 'Anta 'Illā Basharun Mithlunā Wa 'In Nažunnuka Lamina Al-Kādhibīna َ026-186 "Kuma bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu kuma lalle ne munã zaton ka, haƙĩƙa, daga maƙaryata." وَمَا أَنْتَ إِلاَّ بَشَر ٌ مِثْلُنَا وَإِنْ نَظُنُّكَ لَمِنَ الْكَاذِبِينَ
Fa'asqiţ `Alaynā Kisafāan Mina As-Samā'i 'In Kunta Mina Aş-Şādiqīna َ026-187 "To ka jẽfo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga mãsu gaskiya." فَأَسْقِطْ عَلَيْنَا كِسَفا ً مِنَ السَّمَاءِ إِنْ كُنْتَ مِنَ الصَّادِقِينَ
Qāla Rabbī 'A`lamu Bimā Ta`malūna َ026-188 Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa." قَالَ رَبِّي أَعْلَمُ بِمَا تَعْمَلُونَ
Fakadhdhabūhu Fa'akhadhahum `Adhābu Yawmi Až-Žullati  ۚ  'Innahu Kāna `Adhāba Yawmin `Ažīmin َ026-189 Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma. فَكَذَّبُوه ُُ فَأَخَذَهُمْ عَذَابُ يَوْمِ الظُّلَّةِ  ۚ  إِنَّه ُُ كَانَ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيم ٍ
'Inna Fī Dhālika La'āyatan  ۖ  Wa Mā Kāna 'Aktharuhum Mu'uminīna َ026-190 Lalle a cikin wancan haƙĩka akwai ãya, amma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba. إِنَّ فِي ذَلِكَ لَآيَة ً  ۖ  وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُمْ مُؤْمِنِينَ
Wa 'Inna Rabbaka Lahuwa Al-`Azīzu Ar-Raĥīmu َ026-191 Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai. وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Wa 'Innahu Latanzīlu Rabbi Al-`Ālamīna َ026-192 Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne. وَإِنَّه ُُ لَتَنْزِيلُ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Nazala Bihi Ar-Rūĥu Al-'Amīnu َ026-193 Rũhi amintacce ne ya sauka da shi. نَزَلَ بِهِ الرُّوحُ الأَمِينُ
`Alá Qalbika Litakūna Mina Al-Mundhirīna َ026-194 A kan zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi. عَلَى قَلْبِكَ لِتَكُونَ مِنَ الْمُنذِرِينَ
Bilisānin `Arabīyin Mubīnin َ026-195 Da harshe na Larabci mai bayãni. بِلِسَانٍ عَرَبِيّ ٍ مُبِين ٍ
Wa 'Innahu Lafī Zuburi Al-'Awwalīna َ026-196 Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko. وَإِنَّه ُُ لَفِي زُبُرِ الأَوَّلِينَ
'Awalam Yakun Lahum 'Āyatan 'An Ya`lamahu `Ulamā'u Banī 'Isrā'īla َ026-197 Ashe, bai kasance ãyã ba a gare su, ya zama Mãlaman Banĩ Isrã'ĩla sun san shi? أَوَلَمْ يَكُنْ لَهُمْ آيَةً أَنْ يَعْلَمَه ُُ عُلَمَاءُ بَنِي إِسْرَائِيلَ
Wa Law Nazzalnāhu `Alá Ba`đi Al-'A`jamīna َ026-198 Kuma dã mun saukar da shi a kan sãshen Ajamãwa, وَلَوْ نَزَّلْنَاه ُُ عَلَى بَعْضِ الأَعْجَمِينَ
Faqara'ahu `Alayhim Mā Kānū Bihi Mu'uminīna َ026-199 Ya karanta shi a kansu, ba su kasance sabõda shi mãsu ĩmãni ba. فَقَرَأَه ُُ عَلَيْهِمْ مَا كَانُوا بِه ِِ مُؤْمِنِينَ
Kadhālika Salaknāhu Fī Qulūbi Al-Mujrimīna َ026-200 Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi. كَذَلِكَ سَلَكْنَاه ُُ فِي قُلُوبِ الْمُجْرِمِينَ
Lā Yu'uminūna Bihi Ĥattá Yaraw Al-`Adhāba Al-'Alīma َ026-201 Bã zã su yi ĩmãni da shĩ ba sai sun ga azãbar nan mai raɗadi. لاَ يُؤْمِنُونَ بِه ِِ حَتَّى يَرَوْا الْعَذَابَ الأَلِيمَ
Faya'tiyahum Baghtatan Wa Hum Lā Yash`urūna َ026-202 Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba. فَيَأْتِيَهُمْ بَغْتَة ً وَهُمْ لاَ يَشْعُرُونَ
Fayaqūlū Hal Naĥnu Munžarūna َ026-203 Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?" فَيَقُولُوا هَلْ نَحْنُ مُنظَرُونَ
'Afabi`adhābinā Yasta`jilūna َ026-204 Ashe, to, da azãbarMu suke nẽman gaggãwa? أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ
'Afara'ayta 'In Matta`nāhum Sinīna َ026-205 Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru, أَفَرَأَيْتَ إِنْ مَتَّعْنَاهُمْ سِنِينَ
Thumma Jā'ahum Mā Kānū Yū`adūna َ026-206 Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu, ثُمَّ جَاءَهُمْ مَا كَانُوا يُوعَدُونَ
Mā 'Aghná `Anhum Mā Kānū Yumatta`ūna َ026-207 Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare su. مَا أَغْنَى عَنْهُمْ مَا كَانُوا يُمَتَّعُونَ
Wa Mā 'Ahlaknā Min Qaryatin 'Illā Lahā Mundhirūna َ026-208 Kuma bã Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da mãsu gargaɗi. وَمَا أَهْلَكْنَا مِنْ قَرْيَة ٍ إِلاَّ لَهَا مُنذِرُونَ
Dhikrá Wa Mā Kunnā Žālimīna َ026-209 Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba. ذِكْرَى وَمَا كُنَّا ظَالِمِينَ
Wa Mā Tanazzalat Bihi Ash-Shayāţīnu َ026-210 Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba. وَمَا تَنَزَّلَتْ بِهِ الشَّيَاطِينُ
Wa Mā Yanbaghī Lahum Wa Mā Yastaţī`ūna َ026-211 Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa. وَمَا يَنْبَغِي لَهُمْ وَمَا يَسْتَطِيعُونَ
'Innahum `Ani As-Sam`i Lama`zūlūna َ026-212 Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne. إِنَّهُمْ عَنِ السَّمْعِ لَمَعْزُولُونَ
Falā Tad`u Ma`a Al-Lahi 'Ilahāan 'Ākhara Fatakūna Mina Al-Mu`adhdhabīna َ026-213 Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba. فَلاَ تَدْعُ مَعَ اللَّهِ إِلَها ً آخَرَ فَتَكُونَ مِنَ الْمُعَذَّبِينَ
Wa 'Andhir `Ashīrataka Al-'Aqrabīna َ026-214 Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci. وَأَنذِرْ عَشِيرَتَكَ الأَقْرَبِينَ
Wa Akhfiđ Janāĥaka Limani Attaba`aka Mina Al-Mu'uminīna َ026-215 Kuma ka sassauta fikãfikanka ga wanda ya bĩ ka daga mũminai. وَاخْفِضْ جَنَاحَكَ لِمَنِ اتَّبَعَكَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ
Fa'in `Aşawka Faqul 'Innī Barī'un Mimmā Ta`malūna َ026-216 Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa." فَإِنْ عَصَوْكَ فَقُلْ إِنِّي بَرِيء ٌ مِمَّا تَعْمَلُونَ
Wa Tawakkal `Alá Al-`Azīzi Ar-Raĥīmi َ026-217 Kuma ka dõgara ga Mabuwãyi, Mai jin ƙai. وَتَوَكَّلْ عَلَى الْعَزِيزِ الرَّحِيمِ
Al-Ladhī Yarāka Ĥīna Taqūmu َ026-218 Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye. الَّذِي يَرَاكَ حِينَ تَقُومُ
Wa Taqallubaka Fī As-Sājidīna َ026-219 Da jujjuyãwarka a cikin mãsu yin sujada. وَتَقَلُّبَكَ فِي السَّاجِدِينَ
'Innahu Huwa As-Samī`u Al-`Alīmu َ026-220 Lalle Shi, Shi ne Mai ji,Masani. إِنَّه ُُ هُوَ السَّمِيعُ الْعَلِيمُ
Hal 'Unabbi'ukum `Alá Man Tanazzalu Ash-Shayāţīnu َ026-221 Shin, (kunã so) in gaya muku a kan wanda Shaiɗãnnu kan sauka? هَلْ أُنَبِّئُكُمْ عَلَى مَنْ تَنَزَّلُ الشَّيَاطِينُ
Tanazzalu `Alá Kulli 'Affākin 'Athīmin َ026-222 Sukan sauka a kan dukkan maƙaryaci, mai zunubi. تَنَزَّلُ عَلَى كُلِّ أَفَّاكٍ أَثِيم ٍ
Yulqūna As-Sam`a Wa 'Aktharuhumdhibūna َ026-223 Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne. يُلْقُونَ السَّمْعَ وَأَكْثَرُهُمْ كَاذِبُونَ
Wa Ash-Shu`arā'u Yattabi`uhumu Al-Ghāwūna َ026-224 Kuma mawãƙa halakakku ne ke bin su. وَالشُّعَرَاءُ يَتَّبِعُهُمُ الْغَاوُونَ
'Alam Tará 'Annahum Fī Kulli Wādin Yahīmūna َ026-225 Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba? أَلَمْ تَرَى أَنَّهُمْ فِي كُلِّ وَاد ٍ يَهِيمُونَ
Wa 'Annahum Yaqūlūna Mā Lā Yaf`alūna َ026-226 Kuma lalle ne, sũ, sunã faɗin abin da bã su aikatãwa? وَأَنَّهُمْ يَقُولُونَ مَا لاَ يَفْعَلُونَ
'Illā Al-Ladhīna 'Āmanū Wa `Amilū Aş-Şāliĥāti Wa Dhakarū Al-Laha Kathīrāan Wa Antaşarū Min Ba`di Mā Žulimū  ۗ  Wa Saya`lamu Al-Ladhīna Žalamū 'Ayya Munqalabin Yanqalibūna َ026-227 Fãce waɗanda suka yi ĩmãni suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka ambaci Allah da yawa, kuma suka rãma zãlunci, daga bãyan an zãlunce su. Kuma waɗanda suka yi zãlunci, zã su sani a wace majũya suke jũyãwa. إِلاَّ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ وَذَكَرُوا اللَّهَ كَثِيرا ً وَانتَصَرُوا مِنْ بَعْدِ مَا ظُلِمُوا  ۗ  وَسَيَعْلَمُ الَّذِينَ ظَلَمُوا أَيَّ مُنقَلَب ٍ يَنقَلِبُونَ
Next Sūrah