18) Sūrat Al-Kahf

Printed format

18) سُورَة الكَهف

Al-Ĥamdu Lillahi Al-Ladhī 'Anzala `Alá `Abdihi Al-Kitāba Wa Lam Yaj`al Llahu `Iwajā َ018-001 Gõdiya ta tabbata ga Allah wanda Ya saukar da Littafi a kan bãwansa kuma bai sanya karkata ba a gare shi. الْحَمْدُ لِلَّهِ الَّذِي أَنزَلَ عَلَى عَبْدِهِ الْكِتَابَ وَلَمْ يَجْعَلْ لَّه ُُ عِوَجَا
Qayyimāan Liyundhira Ba'sāan Shadīdāan Min Ladunhu Wa Yubashshira Al-Mu'uminīna Al-Ladhīna Ya`malūna Aş-Şāliĥāti 'Anna Lahum 'Ajrāan Ĥasanāan َ018-002 Madaidaici, dõmin Ya yi gargaɗi da azãba mai tsanani daga gare shi, kuma Ya yi bushãra ga mũminai, waɗanda suke aikata ayyuka na ƙwarai da (cẽwa) sunã da wata lãdã mai kyau. قَيِّما ً لِيُنذِرَ بَأْسا ً شَدِيدا ً مِنْ لَدُنْهُ وَيُبَشِّرَ الْمُؤْمِنِينَ الَّذِينَ يَعْمَلُونَ الصَّالِحَاتِ أَنَّ لَهُمْ أَجْراً حَسَنا ً
Mākithīna Fīhi 'Abadāan َ018-003 Sunã mãsu zama a cikinta har abada. مَاكِثِينَ فِيهِ~ِ أَبَدا ً
Wa Yundhira Al-Ladhīna Qālū Attakhadha Al-Lahu Waladāan َ018-004 Kuma Ya yi gargaɗi ga waɗanda suka ce: "Allah yanã da ɗa." وَيُنذِرَ الَّذِينَ قَالُوا اتَّخَذَ اللَّهُ وَلَدا ً
Mmā Lahum Bihi Min `Ilmin Wa Lā Li'ābā'ihim  ۚ  Kaburat Kalimatan Takhruju Min 'Afwāhihim  ۚ  'In Yaqūlūna 'Illā Kadhibāan َ018-005 Ba su da wani ilmi game da wannan magana, kuma iyãyensu bã su da shi, abin da ke fita daga bãkunansu ya girma ga ya zama kalmar faɗa! Ba su faɗan kõme fãce ƙarya. مَّا لَهُمْ بِه ِِ مِنْ عِلْم ٍ وَلاَ لِآبَائِهِمْ  ۚ  كَبُرَتْ كَلِمَة ً تَخْرُجُ مِنْ أَفْوَاهِهِمْ  ۚ  إِنْ يَقُولُونَ إِلاَّ كَذِبا ً
Fala`allaka Bākhi`un Nafsaka `Alá 'Āthārihim 'In Lam Yu'uminū Bihadhā Al-Ĥadīthi 'Asafāan َ018-006 To, kã yi kusa ka halaka ranka a gurabbansu, wai dõmin ba su yi ĩmãni da wannan lãbãri ba sabõda baƙin ciki. فَلَعَلَّكَ بَاخِع ٌ نَفْسَكَ عَلَى آثَارِهِمْ إِنْ لَمْ يُؤْمِنُوا بِهَذَا الْحَدِيثِ أَسَفا ً
'Innā Ja`alnā Mā `Alá Al-'Arđi Zīnatan Lahā Linabluwahum 'Ayyuhum 'Aĥsanu `Amalāan َ018-007 Lalle ne Mũ, Mun sanya abin da ke kan ƙasa wata ƙawa ce gare ta, dõmin Mu jarraba su; wanne daga cikinsu zai zama mafi kyau ga aiki. إِنَّا جَعَلْنَا مَا عَلَى الأَرْضِ زِينَة ً لَهَا لِنَبْلُوَهُمْ أَيُّهُمْ أَحْسَنُ عَمَلا ً
Wa 'Innā Lajā`ilūna Mā `Alayhā Şa`īdāan Juruzāan َ018-008 Kuma lalle Mũ, Mãsu sanya abin da ke a kanta (ya zama) turɓãya ƙeƙasasshiya ne. وَإِنَّا لَجَاعِلُونَ مَا عَلَيْهَا صَعِيدا ً جُرُزا ً
'Am Ĥasibta 'Anna 'Aşĥāba Al-Kahfi Wa Ar-Raqīmi Kānū Min 'Āyātinā `Ajabāan َ018-009 Ko kuwa kã yi zaton cẽwa ma'abũta kõgo da allo sun kasance abin mãmãki daga ãyõyin Allah? أَمْ حَسِبْتَ أَنَّ أَصْحَابَ الْكَهْفِ وَالرَّقِيمِ كَانُوا مِنْ آيَاتِنَا عَجَبا ً
'Idh 'Awá Al-Fityatu 'Ilá Al-Kahfi Faqālū Rabbanā 'Ātinā Min Ladunka Raĥmatan Wa Hayyi' Lanā Min 'Amrinā Rashadāan َ018-010 A lõkacin da samarin suka tattara zuwa ga kõgon, sai suka ce: "Ya Ubangijinmu! Ka bã mu wata rahama daga gare Ka, kuma Ka sauƙaƙe mana (sãmun) shiriya daga al'amarinmu." إِذْ أَوَى الْفِتْيَةُ إِلَى الْكَهْفِ فَقَالُوا رَبَّنَا آتِنَا مِنْ لَدُنْكَ رَحْمَة ً وَهَيِّئْ لَنَا مِنْ أَمْرِنَا رَشَدا ً
Fađarabnā `Alá 'Ādhānihim Al-Kahfi Sinīna `Adadāan َ018-011 Sai Muka yi dũka a kan kunnunwansu, a cikin kõgon, shẽkaru mãsu yawa. فَضَرَبْنَا عَلَى آذَانِهِمْ فِي الْكَهْفِ سِنِينَ عَدَدا ً
Thumma Ba`athnāhum Lina`lama 'Ayyu Al-Ĥizbayni 'Aĥşá Limā Labithū 'Amadāan َ018-012 Sa'an nan Muka tãyar da su, dõmin Mu san wane ɗayan ƙungiyõyin biyu suka fi lissãfi ga abin da suka zauna na lõkacin. ثُمَّ بَعَثْنَاهُمْ لِنَعْلَمَ أَيُّ الْحِزْبَيْنِ أَحْصَى لِمَا لَبِثُوا أَمَدا ً
Naĥnu Naquşşu `Alayka Naba'ahum Bil-Ĥaqqi  ۚ  'Innahum Fityatun 'Āmanū Birabbihim Wa Zidnāhum Hudáan َ018-013 Mu ne ke jẽranta maka lãbãrinsu da gaskiya. Lalle ne sũ, waɗansu samãri ne. Sun yi ĩmãni da Ubangijinsu, kuma Muka ƙãra musu wata shiriya. نَحْنُ نَقُصُّ عَلَيْكَ نَبَأَهُمْ بِالْحَقِّ  ۚ  إِنَّهُمْ فِتْيَة ٌ آمَنُوا بِرَبِّهِمْ وَزِدْنَاهُمْ هُدى ً
Wa Rabaţnā `Alá Qulūbihim 'Idh Qāmū Faqālū Rabbunā Rabbu As-Samāwāti Wa Al-'Arđi Lan Nad`uwa Min Dūnihi 'Ilahāan  ۖ  Laqad Qulnā 'Idhāan Shaţaţāan َ018-014 Kuma Muka ɗaure a kan zukãtansu, a lõkacin da suka tsayu, sa'an nan suka ce: "Ubangijinmu Shĩ ne Ubangijin sammai daƙasa. Bã zã mu kirãyi waninSa abin bautawa ba. (Idan mun yi haka) lalle ne, haƙĩƙa, mun faɗi abin da ya ƙẽtare haddi a sa'an nan." وَرَبَطْنَا عَلَى قُلُوبِهِمْ إِذْ قَامُوا فَقَالُوا رَبُّنَا رَبُّ السَّمَاوَاتِ وَالأَرْضِ لَنْ نَدْعُوَ مِنْ دُونِهِ~ِ إِلَها ً  ۖ  لَقَدْ قُلْنَا إِذا ً شَطَطا ً
Hā'uulā' Qawmunā Attakhadhū Min Dūnihi 'Ālihatan  ۖ  Lawlā Ya'tūna `Alayhim Bisulţānin Bayyinin  ۖ  Faman 'Ažlamu Mimmani Aftará `Alá Al-Lahi Kadhibāan َ018-015 "Ga waɗannan mutãnenmu sun riƙi waninSa abin bautãwa! Don me bã su zuwa da wata hujja bayyananna a kansu (waɗanda ake bautawar) ? To, wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙãga ƙarya ga Allah?" هَاؤُلاَء قَوْمُنَا اتَّخَذُوا مِنْ دُونِهِ آلِهَة ً  ۖ  لَوْلاَ يَأْتُونَ عَلَيْهِمْ بِسُلْطَان ٍ بَيِّن ٍ  ۖ  فَمَنْ أَظْلَمُ مِمَّنِ افْتَرَى عَلَى اللَّهِ كَذِبا ً
Wa 'Idh A`tazaltumūhum Wa Mā Ya`budūna 'Illā Al-Laha Fa'wū 'Ilá Al-Kahfi Yanshur Lakum Rabbukum Min Raĥmatihi Wa Yuhayyi' Lakum Min 'Amrikum Mirfaqāan َ018-016 "Kuma idan kun nĩsance su sũ da abin da suke bautãwa,fãce Allah, to, ku tattara zuwa ga kõgon sai Ubangijinku Ya watsa muku daga rahamarSa kuma Ya sauƙaƙe muku madõgara daga al'amarinku." وَإِذْ اعْتَزَلْتُمُوهُمْ وَمَا يَعْبُدُونَ إِلاَّ اللَّهَ فَأْوُوا إِلَى الْكَهْفِ يَنشُرْ لَكُمْ رَبُّكُمْ مِنْ رَحْمَتِه ِِ وَيُهَيِّئْ لَكُمْ مِنْ أَمْرِكُمْ مِرفَقا ً
Wa Tará Ash-Shamsa 'Idhā Ţala`at Tazāwaru `An Kahfihim Dhāta Al-Yamīni Wa 'Idhā Gharabat Taqriđuhum Dhāta Ash-Shimāli Wa Hum Fī Fajwatin Minhu  ۚ  Dhālika Min 'Āyāti Al-Lahi  ۗ  Man Yahdi Al-Lahu Fahuwa Al-Muhtadi  ۖ  Wa Man Yuđlil Falan Tajida Lahu Walīyāan Murshidāan َ018-017 Kuma kanã ganin rãnã idan ta fito tanã karkata daga kõgonsu wajen dãma kuma idan ta fãɗi tanã gurgura su wajen hagu, kuma su, sunã a cikin wani fili daga gare shi. Wannan abu yanã daga ãyõyin Allah. Wanda Allah Ya shiryar, to shĩ ne mai shiryuwa, kuma wanda Allah Ya ɓatar to bã zã ka sãmar masa wani majiɓinci mai shiryarwa ba. وَتَرَى الشَّمْسَ إِذَا طَلَعَتْ تَزَاوَرُ عَنْ كَهْفِهِمْ ذَاتَ الْيَمِينِ وَإِذَا غَرَبَتْ تَقْرِضُهُمْ ذَاتَ الشِّمَالِ وَهُمْ فِي فَجْوَة ٍ مِنْهُ  ۚ  ذَلِكَ مِنْ آيَاتِ اللَّهِ  ۗ  مَنْ يَهْدِ اللَّهُ فَهُوَ الْمُهْتَدِ  ۖ  وَمَنْ يُضْلِلْ فَلَنْ تَجِدَ لَه ُُ وَلِيّا ً مُرْشِدا ً
Wa Taĥsabuhum 'Ayqāžāan Wa Hum Ruqūdun  ۚ  Wa Nuqallibuhum Dhāta Al-Yamīni Wa Dhāta Ash-Shimāli  ۖ  Wa Kalbuhum Bāsiţun Dhirā`ayhi Bil-Waşīdi  ۚ  Lawi Aţţala`ta `Alayhim Lawallayta Minhum Firārāan Wa Lamuli'ta Minhum Ru`bāan َ018-018 Kuma kanã zaton su farkakku ne, alhãli kuwa sũ mãsu barci ne. Munã jũya su wajen dãma da wajen hagu, kuma karensu yanã shimfiɗe da zirã'õ'in ƙafãfuwansa ga farfãjiya (ta kõgon). Dã ka lẽka (a kan) su (dã) lalle ne, ka jũya daga gare su a guje kuma (dã) lalle ne ka cika da tsõro daga gare su. وَتَحْسَبُهُمْ أَيْقَاظا ً وَهُمْ رُقُود ٌ  ۚ  وَنُقَلِّبُهُمْ ذَاتَ الْيَمِينِ وَذَاتَ الشِّمَالِ  ۖ  وَكَلْبُهُمْ بَاسِط ٌ ذِرَاعَيْهِ بِالْوَصِيدِ  ۚ  لَوِ اطَّلَعْتَ عَلَيْهِمْ لَوَلَّيْتَ مِنْهُمْ فِرَارا ً وَلَمُلِئْتَ مِنْهُمْ رُعْبا ً
Wa Kadhalika Ba`athnāhum Liyatasā'alū Baynahum  ۚ  Qāla Qā'ilun Minhum Kam Labithtum  ۖ  Qālū Labithnā Yawmāan 'Aw Ba`đa Yawmin  ۚ  Qālū Rabbukum 'A`lamu Bimā Labithtumb`athū 'Aĥadakum Biwariqikum Hadhihi 'Ilá Al-Madīnati Falyanžur 'Ayyuhā 'Azká Ţa`āmāan Falya'tikum Birizqin Minhu Wa Līatalaţţaf Wa Lā Yush`iranna Bikum 'Aĥadāan َ018-019 Kuma kamar wannan ne Muka tãyar da su, dõmin su tambayi jũna a tsakãninsu. Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Mẽne ne lõkacin da kuka zauna?" suka ce: "Mun zauna yini ɗaya ko sãshen yini." Suka ce: "Ubangijinku ne Mafi sani ga abin da kuka zauna. To, ku aika da ɗayanku, game da azurfarku wannan, zuwa ga birnin. Sai ya dũba wanne ne mafi tsarki ga abin dafãwa, sai ya zo muku da abinci daga gare shi. Kuma sai ya yi da hankali, kada ya sanar da ku ga wani mutum." وَكَذَلِكَ بَعَثْنَاهُمْ لِيَتَسَاءَلُوا بَيْنَهُمْ  ۚ  قَالَ قَائِل ٌ مِنْهُمْ كَمْ لَبِثْتُمْ  ۖ  قَالُوا لَبِثْنَا يَوْماً أَوْ بَعْضَ يَوْم ٍ  ۚ  قَالُوا رَبُّكُمْ أَعْلَمُ بِمَا لَبِثْتُمْ فَابْعَثُوا أَحَدَكُمْ بِوَرِقِكُمْ هَذِهِ~ِ إِلَى الْمَدِينَةِ فَلْيَنظُرْ أَيُّهَا أَزْكَى طَعَاما ً فَلْيَأْتِكُمْ بِرِزْق ٍ مِنْهُ وَلْيَتَلَطَّفْ وَلاَ يُشْعِرَنَّ بِكُمْ أَحَدا ً
'Innahum 'In Yažharū `Alaykum Yarjumūkum 'Aw Yu`īdūkum Fī Millatihim Wa Lan Tufliĥū 'Idhāan 'Abadāan َ018-020 "Lalle ne sũ idan sun kãmã ku, zã su jẽfẽ ku, kõ kuwa su mayar da ku a cikin addininsu kuma bã zã ku sãmi babban rabo, ba, a sa'an nan har abada." إِنَّهُمْ إِنْ يَظْهَرُوا عَلَيْكُمْ يَرْجُمُوكُمْ أَوْ يُعِيدُوكُمْ فِي مِلَّتِهِمْ وَلَنْ تُفْلِحُوا إِذاً أَبَدا ً
Wa Kadhalika 'A`tharnā `Alayhim Liya`lamū 'Anna Wa`da Al-Lahi Ĥaqqun Wa 'Anna As-Sā`ata Lā Rayba Fīhā 'Idh Yatanāza`ūna Baynahum 'Amrahum  ۖ  Faqālū Abnū `Alayhim Bunyānāan  ۖ  Rabbuhum 'A`lamu Bihim  ۚ  Qāla Al-Ladhīna Ghalabū `Alá 'Amrihim Lanattakhidhanna `Alayhim Masjidāan َ018-021 Kuma kamar wancan ne, Muka nũna su (gare su) dõmin su san lalle wa'adin Allah gaskiya ne, kuma lalle ne Sa'a bãbu shakka a cikinta. A lõkacin da suke jãyayyar al'amarinsu a tsakãninsu sai suka ce: "Ku gina wani gini a kansu, Ubangijinsu ne Mafi sani game da su." Waɗanda suka rinjãya a kan al'amarinsu suka ce: "Lalle mu riƙi masãllãci a kansu." وَكَذَلِكَ أَعْثَرْنَا عَلَيْهِمْ لِيَعْلَمُوا أَنَّ وَعْدَ اللَّهِ حَقّ ٌ وَأَنَّ السَّاعَةَ لاَ رَيْبَ فِيهَا إِذْ يَتَنَازَعُونَ بَيْنَهُمْ أَمْرَهُمْ  ۖ  فَقَالُوا ابْنُوا عَلَيْهِمْ بُنْيَانا ً  ۖ  رَبُّهُمْ أَعْلَمُ بِهِمْ  ۚ  قَالَ الَّذِينَ غَلَبُوا عَلَى أَمْرِهِمْ لَنَتَّخِذَنَّ عَلَيْهِمْ مَسْجِدا ً
Sayaqūlūna Thalāthatun Rābi`uhum Kalbuhum Wa Yaqūlūna Khamsatun Sādisuhum Kalbuhum Rajmāan Bil-Ghaybi  ۖ  Wa Yaqūlūna Sab`atun Wa Thāminuhum Kalbuhum  ۚ  Qul Rabbī 'A`lamu Bi`iddatihim Mā Ya`lamuhum 'Illā Qalīlun  ۗ  Falā Tumāri Fīhim 'Illā Mirā'an Žāhirāan Wa Lā Tastafti Fīhim Minhum 'Aĥadāan َ018-022 Zã su ce: "Uku ne da na huɗunsu karensu."Kuma sunã cẽwa, "Biyar ne da na shidansu karensu," a kan jĩfa a cikin duhu. Kuma sunã cẽwa, "Bakwaine da na takwas ɗinsu karensu."Ka ce: "Ubangijĩna ne Mafi saniga ƙidãyarsu, bãbu wanda ya san su fãce kaɗan."Kada ka yi jãyayya bayyananna. Kuma kada ka yi fatawa ga kõwa daga gare su a cikin al'amarinsu. سَيَقُولُونَ ثَلاَثَة ٌ رَابِعُهُمْ كَلْبُهُمْ وَيَقُولُونَ خَمْسَة ٌ سَادِسُهُمْ كَلْبُهُمْ رَجْما ً بِالْغَيْبِ  ۖ  وَيَقُولُونَ سَبْعَة ٌ وَثَامِنُهُمْ كَلْبُهُمْ  ۚ  قُلْ رَبِّي أَعْلَمُ بِعِدَّتِهِمْ مَا يَعْلَمُهُمْ إِلاَّ قَلِيل ٌ  ۗ  فَلاَ تُمَارِ فِيهِمْ إِلاَّ مِرَاء ً ظَاهِرا ً وَلاَ تَسْتَفْتِ فِيهِمْ مِنْهُمْ أَحَدا ً
Wa Lā Taqūlanna Lishay'in 'Innī Fā`ilun Dhālika Ghadāan َ018-023 Kuma kada lalle ka ce ga wani abu, "Lalle ni, mai aikatãwa ne ga wancan a gõbe." وَلاَ تَقُولَنَّ لِشَيْء ٍ إِنِّي فَاعِل ٌ ذَلِكَ غَدا ً
'Illā 'An Yashā'a Al-Lahu  ۚ  Wa Adhkur Rabbaka 'Idhā Nasīta Wa Qul `Asá 'An Yahdiyani Rabbī Li'qraba Min Hādhā Rashadāan َ018-024 Fãce idan Allah Ya so. Kuma ka ambaci Ubangijinka idan ka manta, kuma ka ce: "¦ammãni ga Ubangijĩna, Ya shiryar da ni ga abin da yake shi ne mafi kusa ga wannan na shiriya." إِلاَّ أَنْ يَشَاءَ اللَّهُ  ۚ  وَاذْكُرْ رَبَّكَ إِذَا نَسِيتَ وَقُلْ عَسَى أَنْ يَهْدِيَنِ رَبِّي لِأقْرَبَ مِنْ هَذَا رَشَدا ً
Wa Labithū Fī Kahfihim Thalātha Miā'atin Sinīna Wa Azdādū Tis`āan َ018-025 Kuma suka zauna a cikin kõgonsu shẽkaru ɗarĩ uku kuma suka daɗa tara. وَلَبِثُوا فِي كَهْفِهِمْ ثَلاَثَ مِائَة ٍ سِنِينَ وَازْدَادُوا تِسْعا ً
Quli Al-Lahu 'A`lamu Bimā Labithū  ۖ  Lahu Ghaybu As-Samāwāti Wa Al-'Arđi  ۖ  'Abşir Bihi Wa 'Asmi`  ۚ  Mā Lahum Min Dūnihi Min Wa Līyin Wa Lā Yushriku Fī Ĥukmihi 'Aĥadāan َ018-026 Ka ce: "Allah ne Mafi sani ga abin da suka zauna. Shĩ ne da (sanin) gaibin sammai da ƙasa. Mũne ne ya yi ganinSa da jinSa! Bã su da wani majiɓinci baicinSa kuma bã Ya tãrayya da kõwa a cikin hukuncinsa." قُلِ اللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا لَبِثُوا  ۖ  لَه ُُ غَيْبُ السَّمَاوَاتِ وَالأَرْضِ  ۖ  أَبْصِرْ بِه ِِ وَأَسْمِعْ  ۚ  مَا لَهُمْ مِنْ دُونِه ِِ مِنْ وَلِيّ ٍ وَلاَ يُشْرِكُ فِي حُكْمِهِ~ِ أَحَدا ً
Wa Atlu Mā 'Ūĥiya 'Ilayka Min Kitābi Rabbika  ۖ  Lā Mubaddila Likalimātihi Wa Lan Tajida Min Dūnihi Multaĥadāan َ018-027 Ka karanta abin da aka yi wahayi zuwa gare ka, na littãfin Ubangijinka. Bãbu mai musanyãwa ga kalmõminSa kuma bã zã kã sãmi wata madõgara ba daga waninsa. وَاتْلُ مَا أُوحِيَ إِلَيْكَ مِنْ كِتَابِ رَبِّكَ  ۖ  لاَ مُبَدِّلَ لِكَلِمَاتِه ِِ وَلَنْ تَجِدَ مِنْ دُونِه ِِ مُلْتَحَدا ً
Wa Aşbir Nafsaka Ma`a Al-Ladhīna Yad`ūna Rabbahum Bil-Ghadāati Wa Al-`Ashīyi Yurīdūna Wajhahu Wa Lā  ۖ  Ta`du `Aynāka `Anhum Turīdu Zīnata Al-Ĥayāati Ad-Dunyā Wa Lā  ۖ  Tuţi` Man 'Aghfalnā Qalbahu `An Dhikrinā Wa Attaba`a Hawāhu Wa Kāna 'Amruhu Furuţāan َ018-028 Ka haƙurtar da ranka tãre da waɗanda ke kiran Ubangijinsu, sãfe da maraice, sunã nufin yardarSa. Kuma kada idãnunka su jũya daga barinsu, kanã nufin ƙawar rãyuwar dũniya. Kuma kada ka biwanda Muka shagaltar da zũciyarsa daga hukuncinMu, kuma ya bi son zuciyarsa, alhãli kuwa al'amarinsa ya kasance yin ɓarna. وَاصْبِرْ نَفْسَكَ مَعَ الَّذِينَ يَدْعُونَ رَبَّهُمْ بِالْغَدَاةِ وَالْعَشِيِّ يُرِيدُونَ وَجْهَه ُُ  ۖ  وَلاَ تَعْدُ عَيْنَاكَ عَنْهُمْ تُرِيدُ زِينَةَ الْحَيَاةِ الدُّنْيَا  ۖ  وَلاَ تُطِعْ مَنْ أَغْفَلْنَا قَلْبَه ُُ عَنْ ذِكْرِنَا وَاتَّبَعَ هَوَاه ُُ وَكَانَ أَمْرُه ُُ فُرُطا ً
Wa Quli Al-Ĥaqqu Min Rabbikum  ۖ  Faman Shā'a Falyu'umin Wa Man Shā'a Falyakfur  ۚ  'Innā 'A`tadnā Lilžžālimīna Nārāan 'Aĥāţa Bihim Surādiquhā  ۚ  Wa 'In Yastaghīthū Yughāthū Bimā'in Kālmuhli Yash Al-Wujūha  ۚ  Bi'sa Ash-Sharābu Wa Sā'at Murtafaqāan َ018-029 Kuma ka ce: "Gaskiya daga Ubangijinku take." Sabõda haka wanda ya so, to, ya yi ĩmãni, kuma wanda ya so, to, ya kãfirta. Lalle ne Mũ, Mun yi tattali dõmin azzãlumai wata wuta wadda shãmakunta, sun ƙẽwaye da su. Kuma idan sun nẽmi taimako sai a taimake su da wani ruwa kamar dabzar mai, yanã sõye fuskõki. Tir da abin shansu, kuma wutar ta yi mũnin zama mahũtarsu. وَقُلِ الْحَقُّ مِنْ رَبِّكُمْ  ۖ  فَمَنْ شَاءَ فَلْيُؤْمِنْ وَمَنْ شَاءَ فَلْيَكْفُرْ  ۚ  إِنَّا أَعْتَدْنَا لِلظَّالِمِينَ نَاراً أَحَاطَ بِهِمْ سُرَادِقُهَا  ۚ  وَإِنْ يَسْتَغِيثُوا يُغَاثُوا بِمَاء ٍ كَالْمُهْلِ يَشْوِي الْوُجُوه ََ  ۚ  بِئْسَ الشَّرَابُ وَسَاءَتْ مُرْتَفَقا ً
'Inna Al-Ladhīna 'Āmanū Wa `Amilū Aş-Şāliĥāti 'Innā Lā Nuđī`u 'Ajra Man 'Aĥsana `Amalāan َ018-030 Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai lalle ne Mũ bã Mu tõzartar da lãdar wanda ya kyautata aiki. إِنَّ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ إِنَّا لاَ نُضِيعُ أَجْرَ مَنْ أَحْسَنَ عَمَلا ً
'Ūlā'ika Lahum Jannātu `Adnin Tajrī Min Taĥtihimu Al-'Anhāru Yuĥallawna Fīhā Min 'Asāwira Min Dhahabin Wa Yalbasūna Thiyābāan Khuđrāan Min Sundusin Wa 'Istabraqin Muttaki'īna Fīhā `Alá Al-'Arā'iki  ۚ  Ni`ma Ath-Thawābu Wa Ĥasunat Murtafaqāan َ018-031 Waɗannan sunã da gidãjen Aljannar zama, ƙõramu na gudãna daga ƙarƙashinsu, anã sanya musu ƙawa, a cikinsu, daga mundãye na zinariya, kuma sunã tufantar waɗansu tũfãfi kõre, na alharĩni raƙĩƙi da alharini mai kauri sunã kishingiɗe a cikinsu,a kan, karagu. Mãdalla da sakamakonsu. Kuma Aljanna ta kyautatu da zama wurin hutãwa. أُوْلَائِكَ لَهُمْ جَنَّاتُ عَدْن ٍ تَجْرِي مِنْ تَحْتِهِمُ الأَنْهَارُ يُحَلَّوْنَ فِيهَا مِنْ أَسَاوِرَ مِنْ ذَهَب ٍ وَيَلْبَسُونَ ثِيَاباً خُضْرا ً مِنْ سُندُس ٍ وَإِسْتَبْرَق ٍ مُتَّكِئِينَ فِيهَا عَلَى الأَرَائِكِ  ۚ  نِعْمَ الثَّوَابُ وَحَسُنَتْ مُرْتَفَقا ً
Wa Ađrib Lahum Mathalāan Rajulayni Ja`alnā Li'ĥadihimā Jannatayni Min 'A`nābin Wa Ĥafafnāhumā Binakhlin Wa Ja`alnā Baynahumā Zar`āan َ018-032 Kuma ka buga musu misãli da waɗansu maza biyu. Mun sanya wa ɗayansu gõnaki biyu na inabõbi, kuma Muka kẽwayesu da itãcen dabĩnai, kuma Muka sanya shũka a tsakãninsu (sũ gõnakin). وَاضْرِبْ لَهُمْ مَثَلا ً رَجُلَيْنِ جَعَلْنَا لِأحَدِهِمَا جَنَّتَيْنِ مِنْ أَعْنَاب ٍ وَحَفَفْنَاهُمَا بِنَخْل ٍ وَجَعَلْنَا بَيْنَهُمَا زَرْعا ً
Kiltā Al-Jannatayni 'Ātat 'Ukulahā Wa Lam Tažlim Minhu Shay'āan  ۚ  Wa Fajjarnā Khilālahumā Naharāan َ018-033 Kõwace gõna daga biyun, tã bãyar da amfãninta, kuma ba ta yi zãluncin kõme ba daga gare shi. Kuma Muka ɓuɓɓugar da ƙoramu a tsakãninsu. كِلْتَا الْجَنَّتَيْنِ آتَتْ أُكُلَهَا وَلَمْ تَظْلِمْ مِنْهُ شَيْئا ً  ۚ  وَفَجَّرْنَا خِلاَلَهُمَا نَهَرا ً
Wa Kāna Lahu Thamarun Faqāla Lişāĥibihi Wa Huwa Yuĥāwiruhu 'Anā 'Aktharu Minka Mālāan Wa 'A`azzu Nafarāan َ018-034 Kuma ɗan ĩtãce ya kasance gare shi. Sai ya ce wa abõkinsa, alhali kuwa yanã muhãwara da shi, "Nĩ ne mafĩfĩci daga gare ka a wajen dũkiya, kuma mafi izza a wajen jama'a." وَكَانَ لَه ُُ ثَمَر ٌ فَقَالَ لِصَاحِبِه ِِ وَهُوَ يُحَاوِرُهُ~ُ أَنَا أَكْثَرُ مِنْكَ مَالا ً وَأَعَزُّ نَفَرا ً
Wa Dakhala Jannatahu Wa Huwa Žālimun Linafsihi Qāla Mā 'Ažunnu 'An Tabīda Hadhihi 'Abadāan َ018-035 Kuma ya shiga gõnarsa, alhãli yanã mai zãlunci ga kansa, ya ce: "Bã ni zaton wannan zã ta halaka har abada." وَدَخَلَ جَنَّتَه ُُ وَهُوَ ظَالِم ٌ لِنَفْسِه ِِ قَالَ مَا أَظُنُّ أَنْ تَبِيدَ هَذِهِ~ِ أَبَدا ً
Wa Mā 'Ažunnu As-Sā`ata Qā'imatan Wa La'in Rudidtu 'Ilá Rabbī La'ajidanna Khayrāan Minhā Munqalabāan َ018-036 "Kuma bã ni zaton sa'a mai tsayuwa ce, kuma lalle ne, idan an mayar da ni zuwa ga Ubangijiĩna, to, lalle ne, zan sãmi abin da yake mafi alhẽri daga gare ta ya zama makõma." وَمَا أَظُنُّ السَّاعَةَ قَائِمَة ً وَلَئِنْ رُدِدْتُ إِلَى رَبِّي لَأَجِدَنَّ خَيْرا ً مِنْهَا مُنقَلَبا ً
Qāla Lahu Şāĥibuhu Wa Huwa Yuĥāwiruhu 'Akafarta Bial-Ladhī Khalaqaka Min Turābin Thumma Min Nuţfatin Thumma Sawwāka Rajulāan َ018-037 Abõkinsa ya ce masa, alhãli kuwa yanã muhãwara da shi, "Ashe kã kãfirta da wanda Ya halitta ka daga turɓaya, sa'an nan daga ɗigon maniyi, sa,an nan Ya daidaita ka, ka zama mutum?" قَالَ لَه ُُ صَاحِبُه ُُ وَهُوَ يُحَاوِرُهُ~ُ أَكَفَرْتَ بِالَّذِي خَلَقَكَ مِنْ تُرَاب ٍ ثُمَّ مِنْ نُطْفَة ٍ ثُمَّ سَوَّاكَ رَجُلا ً
Lakinnā Huwa Al-Lahu Rabbī Wa Lā 'Ushriku Birabbī 'Aĥadāan َ018-038 "Amma ni, shĩ ne Allah Ubangijina, kuma bã zan tãra kõwa da Ubangijina ba" لَكِنَّا هُوَ اللَّهُ رَبِّي وَلاَ أُشْرِكُ بِرَبِّي أَحَدا ً
Wa Lawlā 'Idh Dakhalta Jannataka Qulta Mā Shā'a Al-Lahu Lā Qūwata 'Illā Bil-Lahi  ۚ  'In Tarani 'Anā 'Aqalla Minka Mālāan Wa Waladāan َ018-039 "Kuma don me, a lõkacin da ka shiga gõnarka, ka, ce, 'Abin da Allah ya so (shi ke tabbata) bãbu wani ƙarfi fãce game da Allah.' Idan ka gan ni, ni ne mafi ƙaranci daga gare ka a wajen dũkiya da ɗiya." وَلَوْلاَ إِذْ دَخَلْتَ جَنَّتَكَ قُلْتَ مَا شَاءَ اللَّهُ لاَ قُوَّةَ إِلاَّ بِاللَّهِ  ۚ  إِنْ تَرَنِ أَنَا أَقَلَّ مِنْكَ مَالا ً وَوَلَدا ً
Fa`asá Rabbī 'An Yu'utiyanī Khayrāan Min Jannatika Wa Yursila `Alayhā Ĥusbānāan Mina As-Samā'i Fatuşbiĥa Şa`īdāan Zalaqāan َ018-040 "To, akwai fãtan Ubangijĩna Ya ba ni abin da yake mafi alhẽri daga gõnarka, kuma ya aika azãba a kanta (ita gõnarka) daga sama, sai ta wãyi gari turɓãya mai santsi." فَعَسَى رَبِّي أَنْ يُؤْتِيَنِي خَيْرا ً مِنْ جَنَّتِكَ وَيُرْسِلَ عَلَيْهَا حُسْبَانا ً مِنَ السَّمَاءِ فَتُصْبِحَ صَعِيدا ً زَلَقا ً
'Aw Yuşbiĥa Mā'uuhā Ghawrāan Falan Tastaţī`a Lahu Ţalabāan َ018-041 "Kõ kuma ruwanta ya wãyi gari faƙaƙƙe, sabõda haka, bã zã ka iya nẽmo shi ba dõminta." أَوْ يُصْبِحَ مَاؤُهَا غَوْرا ً فَلَنْ تَسْتَطِيعَ لَه ُُ طَلَبا ً
Wa 'Uĥīţa Bithamarihi Fa'aşbaĥa Yuqallibu Kaffayhi `Alá Mā 'Anfaqa Fīhā Wa Hiya Khāwiyatun `Alá `Urūshihā Wa Yaqūlu Yā Laytanī Lam 'Ushrik Birabbī 'Aĥadāan َ018-042 Kuma aka halaka dukan 'ya'yan itãcensa, sai ya wãyi gari yanã jũyar da tãfunansa biyu, sabõda abin da ya kashe a cikinta, alhãli kuwa ita tanã kwance a kan rassanta, kuma yanã cẽwa, "Kaitõna, dã dai ban tãra wani da Ubangijina ba!" وَأُحِيطَ بِثَمَرِه ِِ فَأَصْبَحَ يُقَلِّبُ كَفَّيْهِ عَلَى مَا أَنفَقَ فِيهَا وَهِيَ خَاوِيَةٌ عَلَى عُرُوشِهَا وَيَقُولُ يَالَيْتَنِي لَمْ أُشْرِكْ بِرَبِّي أَحَدا ً
Wa Lam Takun Lahu Fi'atun Yanşurūnahu Min Dūni Al-Lahi Wa Mā Kāna Muntaşirāan َ018-043 Kuma wata jama'a ba ta kasance a gare shi ba, waɗanda ke taimakon sa, baicin Allah, kuma bai kasance mai taimakon kansa ba. وَلَمْ تَكُنْ لَه ُُ فِئَة ٌ يَنصُرُونَه ُُ مِنْ دُونِ اللَّهِ وَمَا كَانَ مُنتَصِرا ً
Hunālika Al-Walāyatu Lillahi Al-Ĥaqqi  ۚ  Huwa Khayrun Thawābāan Wa Khayrun `Uqan َ018-044 A can taimako da jiɓinta ga Allah yake. Shĩ ne kawai Gaskiya, shĩ ne Mafĩfĩci ga lãda kumaMafĩ fĩci ga ãƙiba. هُنَالِكَ الْوَلاَيَةُ لِلَّهِ الْحَقِّ  ۚ  هُوَ خَيْر ٌ ثَوَابا ً وَخَيْرٌ عُقْبا ً
Wa Ađrib Lahum Mathala Al-Ĥayāati Ad-Dunyā Kamā'in 'Anzalnāhu Mina As-Samā'i Fākhtalaţa Bihi Nabātu Al-'Arđi Fa'aşbaĥa Hashīmāan Tadhrūhu Ar-Riyāĥu  ۗ  Wa Kāna Al-Lahu `Alá Kulli Shay'in Muqtadirāan َ018-045 Ka buga musu misãlin rãyuwar dũniya, kamar ruwane wanda Muka saukar da shi daga sama sa'an nan tsirin ƙasa ya garwaya da shi, sa'an nan ya wãyi gari dudduga, iska tanã shiƙar sa. Kuma Allah Ya kasance Mai yawan ĩkon yi ne a kan dukan kõme. وَاضْرِبْ لَهُمْ مَثَلَ الْحَيَاةِ الدُّنْيَا كَمَاءٍ أَنزَلْنَاه ُُ مِنَ السَّمَاءِ فَاخْتَلَطَ بِه ِِ نَبَاتُ الأَرْضِ فَأَصْبَحَ هَشِيما ً تَذْرُوهُ الرِّيَاحُ  ۗ  وَكَانَ اللَّهُ عَلَى كُلِّ شَيْء ٍ مُقْتَدِرا ً
Al-Mālu Wa Al-Banūna Zīnatu Al-Ĥayāati Ad-Dunyā Wa  ۖ  Al-Bāqiyātu Aş-Şāliĥātu Khayrun `Inda Rabbika Thawābāan Wa Khayrun 'Amalāan َ018-046 Dũkiya da ɗiya, sũ ne ƙawar rãyuwar dũniya, kuma ayyuka mãsu wanzuwa na ƙwarai sun fi zama alhẽri a wurin Ubangijinka ga lãda kuma sun fi alhẽri ga bũri. الْمَالُ وَالْبَنُونَ زِينَةُ الْحَيَاةِ الدُّنْيَا  ۖ  وَالْبَاقِيَاتُ الصَّالِحَاتُ خَيْرٌ عِنْدَ رَبِّكَ ثَوَابا ً وَخَيْرٌ أَمَلا ً
Wa Yawma Nusayyiru Al-Jibāla Wa Tará Al-'Arđa Bārizatan Wa Ĥasharnāhum Falam Nughādir Minhum 'Aĥadāan َ018-047 Kuma a rãnar da Muke tafiyar da duwãtsu, kuma ka ga ƙasa bayyane, kuma Mu tãra su har ba Mu bar kõwa ba daga gare su. وَيَوْمَ نُسَيِّرُ الْجِبَالَ وَتَرَى الأَرْضَ بَارِزَة ً وَحَشَرْنَاهُمْ فَلَمْ نُغَادِرْ مِنْهُمْ أَحَدا ً
Wa `Uriđū `Alá Rabbika Şaffāan Laqad Ji'tumūnā Kamā Khalaqnākum 'Awwala Marratin  ۚ  Bal Za`amtum 'Allan Naj`ala Lakum Maw`idāan َ018-048 Kuma a gittã su ga Ubangijinka sunã sahu guda, (Mu ce musu), "Lalle ne haƙĩƙa kun zo Mana, kamar yadda Muka halitta ku a farkon lõkaci. Ã'a, kun riya cẽwa bã zã Mu sanya mukuwani lõkacin haɗuwa ba." وَعُرِضُوا عَلَى رَبِّكَ صَفّا ً لَقَدْ جِئْتُمُونَا كَمَا خَلَقْنَاكُمْ أَوَّلَ مَرَّة ٍ  ۚ  بَلْ زَعَمْتُمْ أَلَّنْ نَجْعَلَ لَكُمْ مَوْعِدا ً
Wa Wuđi`a Al-Kitābu Fatará Al-Mujrimīna Mushfiqīna Mimmā Fīhi Wa Yaqūlūna Yā Waylatanā Māli Hādhā Al-Kitābi Lā Yughādiru Şaghīratan Wa Lā Kabīratan 'Illā 'Aĥşāhā  ۚ  Wa Wajadū Mā `Amilū Ĥāđirāan  ۗ  Wa Lā Yažlimu Rabbuka 'Aĥadāan َ018-049 Kuma aka aza littãfin ayyuka, sai ka ga mãsu laifi sunã mãsu jin tsõro daga abin da ke cikinsa, kuma sunã cẽwa "Kaitonmu! Mẽne ne ga wannan littãfi, bã ya barin ƙarama, kuma bã ya barin babba, fãce yã ƙididdige ta?" Kuma suka sãmi abin da suka aikata halarce. Kuma Ubangijinka bã Ya zãluntar kõwa. وَوُضِعَ الْكِتَابُ فَتَرَى الْمُجْرِمِينَ مُشْفِقِينَ مِمَّا فِيه ِِ وَيَقُولُونَ يَاوَيْلَتَنَا مَالِ هَذَا الْكِتَابِ لاَ يُغَادِرُ صَغِيرَة ً وَلاَ كَبِيرَة ً إِلاَّ أَحْصَاهَا وَوَجَدُوا  ۚ  مَا عَمِلُوا حَاضِرا ً وَلاَ  ۗ  يَظْلِمُ رَبُّكَ أَحَدا ً
Wa 'Idh Qulnā Lilmalā'ikati Asjudū Li'dama Fasajadū 'Illā 'Iblīsa Kāna Mina Al-Jinni Fafasaqa `An 'Amri Rabbihi  ۗ  'Afatattakhidhūnahu Wa Dhurrīyatahu 'Awliyā'a Min Dūnī Wa Hum Lakum `Adūwun  ۚ  Bi'sa Lilžžālimīna Badalāan َ018-050 Kuma a lõkacin da Muka ce wa malãiku, "Ku yi sujada ga Ãdamu." Sai suka yi sujada fãce Iblĩsa, yã kasance daga aljannu sai ya yi fãsiƙanci ga barin umurnin Ubangijinsa, To fa, ashe, kunã riƙon sa, shi da zũriyarsa, su zama majiɓinta baicin Ni, alhãli kuwa su maƙiya ne a gare ku? Tir da ya zama musanya ga azzãlumai. وَإِذْ قُلْنَا لِلْمَلاَئِكَةِ اسْجُدُوا لِأدَمَ فَسَجَدُوا إِلاَّ إِبْلِيسَ كَانَ مِنَ الْجِنِّ فَفَسَقَ عَنْ أَمْرِ رَبِّهِ~ِ  ۗ  أَفَتَتَّخِذُونَه ُُ وَذُرِّيَّتَهُ~ُ أَوْلِيَاءَ مِنْ دُونِي وَهُمْ لَكُمْ عَدُوّ ٌ  ۚ  بِئْسَ لِلظَّالِمِينَ بَدَلا ً
Mā 'Ash/hadtuhum Khalqa As-Samāwāti Wa Al-'Arđi Wa Lā Khalqa 'Anfusihim Wa Mā Kuntu Muttakhidha Al-Muđillīna `Ađudāan َ018-051 Ban shaida musu halittar sammai da ƙasa ba, kuma ban (shaida musu) halittar rãyukansu ba kuma ban kasance mai riƙon mãsu ɓatarwa (da wani) su zama mataimaka ba. مَا أَشْهَدْتُهُمْ خَلْقَ السَّمَاوَاتِ وَالأَرْضِ وَلاَ خَلْقَ أَنفُسِهِمْ وَمَا كُنتُ مُتَّخِذَ الْمُضِلِّينَ عَضُدا ً
Wa Yawma Yaqūlu Nādū Shurakā'iya Al-Ladhīna Za`amtum Fada`awhum Falam Yastajībū Lahum Wa Ja`alnā Baynahum Mawbiqāan َ018-052 Kuma da rãnar da Allah Yake cẽwa, "Ku kirãyi abõkan tarayyãTa, waɗanda kuka riya." Sai su kirãye su, sai bã zã su karɓa musu ba, kuma Mu sanya Maubiƙa (Mahalaka) a tsakãninsu, وَيَوْمَ يَقُولُ نَادُوا شُرَكَائِيَ الَّذِينَ زَعَمْتُمْ فَدَعَوْهُمْ فَلَمْ يَسْتَجِيبُوا لَهُمْ وَجَعَلْنَا بَيْنَهُمْ مَوْبِقا ً
Wa Ra'á Al-Mujrimūna An-Nāra Fažannū 'Annahum Muwāqi`ūhā Wa Lam Yajidū `Anhā Maşrifāan َ018-053 Kuma mãsu laifi suka ga wutã suka tabbata lalle ne, sũ mãsu, auka mata ne, kuma ba su sãmi majũya ba daga gare ta. وَرَأَى الْمُجْرِمُونَ النَّارَ فَظَنُّوا أَنَّهُمْ مُوَاقِعُوهَا وَلَمْ يَجِدُوا عَنْهَا مَصْرِفا ً
Wa Laqad Şarrafnā Fī Hādhā Al-Qur'āni Lilnnāsi Min Kulli Mathalin  ۚ  Wa Kāna Al-'Insānu 'Akthara Shay'in Jadalāan َ018-054 Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun jujjũya, a cikin wannan Alƙur'ãni, daga kõwane irin misãli ga mutãne (dõmin su gãne, su bi sharĩ'a), kuma mutum yã kasance mafi yawan abu ga jidãli. وَلَقَدْ صَرَّفْنَا فِي هَذَا الْقُرْآنِ لِلنَّاسِ مِنْ كُلِّ مَثَل ٍ  ۚ  وَكَانَ الإِنسَانُ أَكْثَرَ شَيْء ٍ جَدَلا ً
Wa Mā Mana`a An-Nāsa 'An Yu'uminū 'Idh Jā'ahumu Al-Hudá Wa Yastaghfirū Rabbahum 'Illā 'An Ta'tiyahum Sunnatu Al-'Awwalīna 'Aw Ya'tiyahumu Al-`Adhābu Qubulāan َ018-055 Kuma bãbu abin da ya hana mutãne su yi ĩmãni a lõkacinda shiriya ta zo musu, kuma su nẽmi gãfara daga Ubangijinsu, fãce hanyar farko ta je musu kõ kuma azãba ta jẽ musu nau'i-nau'i. وَمَا مَنَعَ النَّاسَ أَنْ يُؤْمِنُوا إِذْ جَاءَهُمُ الْهُدَى وَيَسْتَغْفِرُوا رَبَّهُمْ إِلاَّ أَنْ تَأْتِيَهُمْ سُنَّةُ الأَوَّلِينَ أَوْ يَأْتِيَهُمُ الْعَذَابُ قُبُلا ً
Wa Mā Nursilu Al-Mursalīna 'Illā Mubashshirīna Wa Mundhirīna  ۚ  Wa Yujādilu Al-Ladhīna Kafarū Bil-Bāţili Liyudĥiđū Bihi Al-Ĥaqqa  ۖ  Wa Attakhadhū 'Āyātī Wa Mā 'Undhirū Huzūan َ018-056 Kuma ba Mu aika Manzanni ba fãce sunã mãsu bãyar da bushãra kuma mãsu gargaɗi, kuma waɗanda suka kãfirta sunã jidãli da ƙarya dõmin su ɓãta gaskiya da ita, kuma suka riƙi ãyõyiNa da abin da aka yi musu gargaɗi da shi abin izgili. وَمَا نُرْسِلُ الْمُرْسَلِينَ إِلاَّ مُبَشِّرِينَ وَمُنذِرِينَ  ۚ  وَيُجَادِلُ الَّذِينَ كَفَرُوا بِالْبَاطِلِ لِيُدْحِضُوا بِهِ الْحَقَّ  ۖ  وَاتَّخَذُوا آيَاتِي وَمَا أُنْذِرُوا هُزُوا ً
Wa Man 'Ažlamu Mimman Dhukkira Bi'āyāti Rabbihi Fa'a`rađa `Anhā Wa Nasiya Mā Qaddamat Yadāhu  ۚ  'Innā Ja`alnā `Alá Qulūbihim 'Akinnatan 'An Yafqahūhu Wa Fī 'Ādhānihim Waqrāan Wa 'In  ۖ  Tad`uhum 'Ilá Al-Hudá Falan Yahtadū 'Idhāan 'Abadāan َ018-057 Kuma wãne ne mafi zãlunci daga wanda aka tunãtar game da ãyõyin Ubangijinsa, sai ya bijire daga barinsu, kuma ya manta abin da hannãyensa suka gabãtar? Lalle ne Mũ, Mun sanya abũbuwan rufi a kan zukãtansu dõmin kada su fahimcẽ shi, kuma a cikin kunnuwansu (Mun sanya) wani nauyi, kuma idan kã kĩrayẽ su zuwa ga shiriya, to, bã zã su shiryu ba, a sa'an nan, har abada. وَمَنْ أَظْلَمُ مِمَّنْ ذُكِّرَ بِآيَاتِ رَبِّه ِِ فَأَعْرَضَ عَنْهَا وَنَسِيَ مَا قَدَّمَتْ يَدَاهُ~ُ  ۚ  إِنَّا جَعَلْنَا عَلَى قُلُوبِهِمْ أَكِنَّةً أَنْ يَفْقَهُوه ُُ وَفِي آذَانِهِمْ وَقْرا ً  ۖ  وَإِنْ تَدْعُهُمْ إِلَى الْهُدَى فَلَنْ يَهْتَدُوا إِذاً أَبَدا ً
Wa Rabbuka Al-Ghafūru Dhū Ar-Raĥmati  ۖ  Law Yu'uākhidhuhum Bimā Kasabū La`ajjala Lahumu Al-`Adhāba  ۚ  Bal Lahum Maw`idun Lan Yajidū Min Dūnihi Maw'ilāan َ018-058 Kuma Ubangijinka Mai gãfara ne, Ma'abũcin rahama. Dã Yanã kãma su sabõda abin da suka sanã'anta, lalle ne, dã Ya gaggauta azãba a gare su. Ã'a, sunã da lõkacin alkawari,(wanda) bã zã su sãmi wata makõma ba, baicinSa. وَرَبُّكَ الْغَفُورُ ذُو الرَّحْمَةِ  ۖ  لَوْ يُؤَاخِذُهُمْ بِمَا كَسَبُوا لَعَجَّلَ لَهُمُ الْعَذَابَ  ۚ  بَلْ لَهُمْ مَوْعِد ٌ لَنْ يَجِدُوا مِنْ دُونِه ِِ مَوْئِلا ً
Wa Tilka Al-Qurá 'Ahlaknāhum Lammā Žalamū Wa Ja`alnā Limahlikihim Maw`idāan َ018-059 Kuma waɗancan alƙaryu Mun halaka su, a lõkacin da suka yi zãlunci, kuma Muka sanya lõkacin alkawarin, ga halaka su. وَتِلْكَ الْقُرَى أَهْلَكْنَاهُمْ لَمَّا ظَلَمُوا وَجَعَلْنَا لِمَهْلِكِهِمْ مَوْعِدا ً
Wa 'Idh Qāla Mūsá Lifatāhu Lā 'Abraĥu Ĥattá 'Ablugha Majma`a Al-Baĥrayni 'Aw 'Amđiya Ĥuqubāan َ018-060 Kuma a lõkacin da Mũsã ya ce wa yãronsa, "Bã zan gushe ba sai na isa mahaɗar tẽku biyu, kõ in shũɗe da tafiya shekara da shẽkaru." وَإِذْ قَالَ مُوسَى لِفَتَاهُ لاَ أَبْرَحُ حَتَّى أَبْلُغَ مَجْمَعَ الْبَحْرَيْنِ أَوْ أَمْضِيَ حُقُبا ً
Falammā Balaghā Majma`a Baynihimā Nasiyā Ĥūtahumā Fa Attakhadha Sabīlahu Fī Al-Baĥri Sarabāan َ018-061 To, a lõkacin da suka isa mahaɗar tsakãninsu sai suka manta kĩfinsu, sai ya kãma tafarkinsa a cikin tẽku kamar bĩga. فَلَمَّا بَلَغَا مَجْمَعَ بَيْنِهِمَا نَسِيَا حُوتَهُمَا فَاتَّخَذَ سَبِيلَه ُُ فِي الْبَحْرِ سَرَبا ً
Falammā Jāwazā Qāla Lifatāhu 'Ātinā Ghadā'anā Laqad Laqīnā Min Safarinā Hādhā Naşabāan َ018-062 To, a lõkacin da suka wuce ya ce wa yãronsa, "Ka kãwo mana kãlãcinmu. Lalle ne haƙĩƙa mun haɗu da wahala daga tafiyarmu wannan." فَلَمَّا جَاوَزَا قَالَ لِفَتَاهُ آتِنَا غَدَاءَنَا لَقَدْ لَقِينَا مِنْ سَفَرِنَا هَذَا نَصَبا ً
Qāla 'Ara'ayta 'Idh 'Awaynā 'Ilá Aş-Şakhrati Fa'innī Nasītu Al-Ĥūta Wa Mā 'Ansānīhu 'Illā Ash-Shayţānu 'An 'Adhkurahu  ۚ  Wa Attakhadha Sabīlahu Fī Al-Baĥri `Ajabāan َ018-063 (Yãron) ya ce: "Kã gani! A lõkacin da muka tattara zuwa ga falalen nan to, lalle nĩ, na manta kĩfin, kuma bãbu abin da yamantar da nĩ shi, fãce Shaiɗan,dõmin kada in tuna shi, sai ya kama tafarkinsa a cikin tẽku, da mãmãki!" قَالَ أَرَأَيْتَ إِذْ أَوَيْنَا إِلَى الصَّخْرَةِ فَإِنِّي نَسِيتُ الْحُوتَ وَمَا أَنْسَانِيهُ~ُ إِلاَّ الشَّيْطَانُ أَنْ أَذْكُرَه ُُ  ۚ  وَاتَّخَذَ سَبِيلَه ُُ فِي الْبَحْرِ عَجَبا ً
Qāla Dhālika Mā Kunnā Nabghi  ۚ  Fārtaddā `Alá 'Āthārihimā Qaşaşāan َ018-064 Ya ce: "Wancan ne abin da muka kasance munã biɗã." Sai suka kõma a kan gurãbunsu, sunã bĩbiya. قَالَ ذَلِكَ مَا كُنَّا نَبْغِ  ۚ  فَارْتَدَّا عَلَى آثَارِهِمَا قَصَصا ً
Fawajadā `Abdāan Min `Ibādinā 'Ātaynāhu Raĥmatan Min `Indinā Wa `Allamnāhu Min Ladunnā `Ilmāan َ018-065 Sai suka sãmi wani bãwa daga bãyinMu, Mun bã shi wata rahama daga wurinMu, kuma Mun sanar da shi wani ilmi daga gunMu. فَوَجَدَا عَبْدا ً مِنْ عِبَادِنَا آتَيْنَاه ُُ رَحْمَة ً مِنْ عِنْدِنَا وَعَلَّمْنَاه ُُ مِنْ لَدُنَّا عِلْما ً
Qāla Lahu Mūsá Hal 'Attabi`uka `Alá 'An Tu`allimani Mimmā `Ullimta Rushan َ018-066 Mũsã ya ce masa, "Ko in bĩ ka a kan ka sanar da ni daga abin da aka sanar da kai na shiriya?" قَالَ لَه ُُ مُوسَى هَلْ أَتَّبِعُكَ عَلَى أَنْ تُعَلِّمَنِ مِمَّا عُلِّمْتَ رُشْدا ً
Qāla 'Innaka Lan Tastaţī`a Ma`iya Şaban َ018-067 Ya ce: "Lalle ne kai bã zã ka iya yin haƙuri tãre da nĩ, ba." قَالَ إِنَّكَ لَنْ تَسْتَطِيعَ مَعِيَ صَبْرا ً
Wa Kayfa Taşbiru `Alá Mā Lam Tuĥiţ Bihi Khuban َ018-068 "Kuma yãya zã ka yi haƙuri a kan abin da ba ka kẽwayeda shi ba ga jarrabãwa?" وَكَيْفَ تَصْبِرُ عَلَى مَا لَمْ تُحِطْ بِه ِِ خُبْرا ً
Qāla Satajidunī 'In Shā'a Al-Lahu Şābirāan Wa Lā 'A`şī Laka 'Aman َ018-069 Ya ce: "Za ka sãme ni, in Allah Yã so mai haƙuri kuma bã zan sãɓa maka ba ga wani umurni." قَالَ سَتَجِدُنِي إِنْ شَاءَ اللَّهُ صَابِرا ً وَلاَ أَعْصِي لَكَ أَمْرا ً
Qāla Fa'ini Attaba`tanī Falā Tas'alnī `An Shay'in Ĥattá 'Uĥditha Laka Minhu Dhikrāan َ018-070 Ya ce: "To idan ka bĩ ni to kada ka tambaye ni daga kõme sai na lãbarta maka ambato daga gare shi." قَالَ فَإِنِ اتَّبَعْتَنِي فَلاَ تَسْأَلْنِي عَنْ شَيْءٍ حَتَّى أُحْدِثَ لَكَ مِنْهُ ذِكْرا ً
nţalaqā Ĥattá 'Idhā Rakibā Fī As-Safīnati Kharaqahā  ۖ  Qāla 'Akharaqtahā Litughriqa 'Ahlahā Laqad Ji'ta Shay'āan 'Iman َ018-071 Sai suka tafi har a lõkacin da suka hau a cikin jirgi, ya hũje shi, ya ce, "Kã hũje shi dõmin ya nutsar da mutãnensa? Lalle ne, haƙĩƙa,kã zo da wani babban abu!" فَانطَلَقَا حَتَّى إِذَا رَكِبَا فِي السَّفِينَةِ خَرَقَهَا  ۖ  قَالَ أَخَرَقْتَهَا لِتُغْرِقَ أَهْلَهَا لَقَدْ جِئْتَ شَيْئا ً إِمْرا ً
Qāla 'Alam 'Aqul 'Innaka Lan Tastaţī`a Ma`iya Şaban َ018-072 Ya ce: "Ashe ban ce, lalle kai, bã za ka iya yin haƙuri tãre da ni ba?" قَالَ أَلَمْ أَقُلْ إِنَّكَ لَنْ تَسْتَطِيعَ مَعِيَ صَبْرا ً
Qāla Lā Tu'uākhidhnī Bimā Nasītu Wa Lā Turhiqnī Min 'Amrī `Usrāan َ018-073 Ya ce: "Kada ka kãma ni da abin da na manta kuma kada ka kallafa mini tsanani ga al'amarĩna." قَالَ لاَ تُؤَاخِذْنِي بِمَا نَسِيتُ وَلاَ تُرْهِقْنِي مِنْ أَمْرِي عُسْرا ً
nţalaqā Ĥattá 'Idhā Laqiyā Ghulāmāan Faqatalahu Qāla 'Aqatalta Nafsāan Zakīyatan Bighayri Nafsin Laqad Ji'ta Shay'āan Nukrāan َ018-074 Sai suka tafi, har suka haɗu da wani yãro, sai ya kashe shi. Ya ce: "Ashe kã kashe rai tsarkakakke, bã da wani rai ba? Lalle ne haƙĩƙa ka zo da wani abu na ƙyãma." فَانطَلَقَا حَتَّى إِذَا لَقِيَا غُلاَما ً فَقَتَلَه ُُ قَالَ أَقَتَلْتَ نَفْسا ً زَكِيَّة ً بِغَيْرِ نَفْس ٍ لَقَدْ جِئْتَ شَيْئا ً نُكْرا ً
Qāla 'Alam 'Aqul Laka 'Innaka Lan Tastaţī`a Ma`iya Şaban َ018-075 Ya ce: "Shin, ban ce maka ba, lalle ne kai bã zã ka iya yin haƙuri tãre da nĩ ba?" قَالَ أَلَمْ أَقُلْ لَكَ إِنَّكَ لَنْ تَسْتَطِيعَ مَعِيَ صَبْرا ً
Qāla 'In Sa'altuka `An Shay'in Ba`dahā Falā Tuşāĥibnī  ۖ  Qad Balaghta Min Ladunnī `Udhan َ018-076 Ya ce: "Idan na tambaye ka daga wani abu a bãyanta, to, kada ka abũce ni. Lalle ne, kã isa ga iyakar uzuri daga gare ni." قَالَ إِنْ سَأَلْتُكَ عَنْ شَيْء ٍ بَعْدَهَا فَلاَ تُصَاحِبْنِي  ۖ  قَدْ بَلَغْتَ مِنْ لَدُنِّي عُذْرا ً
nţalaqā Ĥattá 'Idhā 'Atayā 'Ahla Qaryatin Astaţ`amā 'Ahlahā Fa'abaw 'An Yuđayyifūhumā Fawajadā Fīhā Jidārāan Yurīdu 'An Yanqađđa Fa'aqāmahu  ۖ  Qāla Law Shi'ta Lāttakhadhta `Alayhi 'Ajan َ018-077 Sai suka tafi, har a lõkacin da suka je wa mutãnen wata alƙarya, suka nẽmi mutãnenta da su bã su abinci, sai suka ƙi su yi musu liyãfa. Sai suka sãmi wani bango a cikinta yanã nufin ya karye, sai (Halliru) ya tãyar da shi mĩƙe. (Mũsã) ya ce: "Dã kã so, lalle ne dã kã karɓi ijãra a kansa." فَانطَلَقَا حَتَّى إِذَا أَتَيَا أَهْلَ قَرْيَة ٍ اسْتَطْعَمَا أَهْلَهَا فَأَبَوْا أَنْ يُضَيِّفُوهُمَا فَوَجَدَا فِيهَا جِدَارا ً يُرِيدُ أَنْ يَنقَضَّ فَأَقَامَه ُُ  ۖ  قَالَ لَوْ شِئْتَ لاَتَّخَذْتَ عَلَيْهِ أَجْرا ً
Qāla Hādhā Firāqu Baynī Wa Baynika  ۚ  Sa'unabbi'uka Bita'wīli Mā Lam Tastaţi` `Alayhi Şaban َ018-078 Ya ce: "Wannan shi ne rabuwar tsakanina da tsakaninka. Zã ni gaya maka fassarar abin da ba ka iya yin haƙuri ba a kansa." قَالَ هَذَا فِرَاقُ بَيْنِي وَبَيْنِكَ  ۚ  سَأُنَبِّئُكَ بِتَأْوِيلِ مَا لَمْ تَسْتَطِعْ عَلَيْهِ صَبْرا ً
'Ammā As-Safīnatu Fakānat Limasākīna Ya`malūna Fī Al-Baĥri Fa'aradtu 'An 'A`ībahā Wa Kāna Warā'ahum Malikun Ya'khudhu Kulla Safīnatin Ghaşbāan َ018-079 "Amma Jirgin, to, ya zama na waɗansu matalauta ne sunã aiki a cikin tẽku, sai na yi niyyar in aibanta shi, alhãli kuwa wani sarki ya kasance a gaba gare su, yanã karɓẽwar kõwane jirgi (lãfiyayye) da ƙwãce. أَمَّا السَّفِينَةُ فَكَانَتْ لِمَسَاكِينَ يَعْمَلُونَ فِي الْبَحْرِ فَأَرَدْتُ أَنْ أَعِيبَهَا وَكَانَ وَرَاءَهُمْ مَلِك ٌ يَأْخُذُ كُلَّ سَفِينَةٍ غَصْبا ً
Wa 'Ammā Al-Ghulāmu Fakāna 'Abawāhu Mu'uminayni Fakhashīnā 'An Yurhiqahumā Ţughyānāan Wa Kufrāan َ018-080 "Kuma amma yaron, to, uwãyensa sun kasance mũminai, to, sai muka ji tsõron ya kallafa musu kangara da kãfirci." وَأَمَّا الْغُلاَمُ فَكَانَ أَبَوَاه ُُ مُؤْمِنَيْنِ فَخَشِينَا أَنْ يُرْهِقَهُمَا طُغْيَانا ً وَكُفْرا ً
Fa'aradnā 'An Yubdilahumā Rabbuhumā Khayrāan Minhu Zakāatan Wa 'Aqraba Ruĥmāan َ018-081 "Sai muka yi nufin Ubangijinsu Ya musanya musu mafi alhẽri daga gare shi ga tsarkakuwa, kuma mafi kusantar tausayi." فَأَرَدْنَا أَنْ يُبْدِلَهُمَا رَبُّهُمَا خَيْرا ً مِنْهُ زَكَاة ً وَأَقْرَبَ رُحْما ً
Wa 'Ammā Al-Jidāru Fakāna Lighulāmayni Yatīmayni Fī Al-Madīnati Wa Kāna Taĥtahu Kanzun Lahumā Wa Kāna 'Abūhumā Şāliĥāan Fa'arāda Rabbuka 'An Yablughā 'Ashuddahumā Wa Yastakhrijā Kanzahumā Raĥmatan Min Rabbika  ۚ  Wa Mā Fa`altuhu `An 'Amrī  ۚ  Dhālika Ta'wīlu Mā Lam Tasţi` `Alayhi Şaban َ018-082 "Kuma amma bangon, to, yã kasance na waɗansu yãra biyu ne, marãyu a cikin birnin, kuma akwai wata taska tãsu a ƙarƙashinsa, kuma ubansu ya kasance sahĩhin mutum ne, dõmin haka Ubangijinka Ya yi nufin su isa iyãkar ƙarfinsu, kuma sũ, su fitar da taskarsu, sabõda rahama ne daga Ubangijinka. Kuma ban yi shi ba daga umurnĩna. Wancan shĩ ne fassarar abin da ba ka iya yin haƙuri ba a kansa." وَأَمَّا الْجِدَارُ فَكَانَ لِغُلاَمَيْنِ يَتِيمَيْنِ فِي الْمَدِينَةِ وَكَانَ تَحْتَه ُُ كَنز ٌ لَهُمَا وَكَانَ أَبُوهُمَا صَالِحا ً فَأَرَادَ رَبُّكَ أَنْ يَبْلُغَا أَشُدَّهُمَا وَيَسْتَخْرِجَا كَنزَهُمَا رَحْمَة ً مِنْ رَبِّكَ  ۚ  وَمَا فَعَلْتُه ُُ عَنْ أَمْرِي  ۚ  ذَلِكَ تَأْوِيلُ مَا لَمْ تَسْطِعْ عَلَيْهِ صَبْرا ً
Wa Yas'alūnaka `An Dhī Al-Qarnayni  ۖ  Qul Sa'atlū `Alaykum Minhu Dhikrāan َ018-083 Kuma suna tambayar ka daga zulƙarnaini, ka ce: "Zan karanta muku ambato daga gare shi." وَيَسْأَلُونَكَ عَنْ ذِي الْقَرْنَيْنِ  ۖ  قُلْ سَأَتْلُو عَلَيْكُمْ مِنْهُ ذِكْرا ً
'Innā Makkannā Lahu Fī Al-'Arđi Wa 'Ātaynāhu Min Kulli Shay'in Sababāan َ018-084 Lalle ne Mũ Mun bã shi mulki a cikin ƙasa kuma Muka bã shi daga kõwane abu, hanya (zuwa ga murãdinsa). إِنَّا مَكَّنَّا لَه ُُ فِي الأَرْضِ وَآتَيْنَاه ُُ مِنْ كُلِّ شَيْء ٍ سَبَبا ً
Fa'atba`a Sababāan َ018-085 Sai ya bi hanya. فَأَتْبَعَ سَبَبا ً
Ĥattá 'Idhā Balagha Maghriba Ash-Shamsi Wajadahā Taghrubu Fī `Aynin Ĥami'atin Wa Wajada `Indahā Qawmāan  ۗ  Qulnā Yā Dhā Al-Qarnayni 'Immā 'An Tu`adhdhiba Wa 'Immā 'An Tattakhidha Fīhim Ĥusnāan َ018-086 Har a lõkacin da ya isa ga mafãɗar rãnã, kuma ya sãme ta tanã ɓacẽwa a cikin wani ruwa mai baƙar lãkã, kuma ya sãmi waɗansu mutãne a wurinta. Muka ce: "Yã Zulƙarnaini imma dai ka azabtar kuma imma ka riƙi kyautatãwa a cikinsu." حَتَّى إِذَا بَلَغَ مَغْرِبَ الشَّمْسِ وَجَدَهَا تَغْرُبُ فِي عَيْنٍ حَمِئَة ٍ وَوَجَدَ عِنْدَهَا قَوْما ً  ۗ  قُلْنَا يَاذَا الْقَرْنَيْنِ إِمَّا أَنْ تُعَذِّبَ وَإِمَّا أَنْ تَتَّخِذَ فِيهِمْ حُسْنا ً
Qāla 'Ammā Man Žalama Fasawfa Nu`adhdhibuhu Thumma Yuraddu 'Ilá Rabbihi Fayu`adhdhibuhu `Adhābāan Nukrāan َ018-087 Ya ce: "Amma wanda ya yi zãlunci, to zã mu azabta shi, sa'an nan a mayar da shi zuwa ga Ubangijinsa, sai kuma Ya yi masa azãba, azãba abar ƙyãma." قَالَ أَمَّا مَنْ ظَلَمَ فَسَوْفَ نُعَذِّبُه ُُ ثُمَّ يُرَدُّ إِلَى رَبِّه ِِ فَيُعَذِّبُه ُُ عَذَابا ً نُكْرا ً
Wa 'Ammā Man 'Āmana Wa `Amila Şāliĥāan Falahu Jazā'an Al-Ĥusná  ۖ  Wa Sanaqūlu Lahu Min 'Amrinā Yusrāan َ018-088 "Kuma amma wanda ya yi ĩmãni kuma ya aikata aikin ƙwarai to, zã mu yi sakamako a gare shi (watau kyauta) mai kyau, kuma zã mu gaya masa sauƙi daga umurninmu." وَأَمَّا مَنْ آمَنَ وَعَمِلَ صَالِحا ً فَلَه ُُ جَزَاء ً الْحُسْنَى  ۖ  وَسَنَقُولُ لَه ُُ مِنْ أَمْرِنَا يُسْرا ً
Thumma 'Atba`a Sababāan َ018-089 Sa'an nan kuma ya bi hanya. ثُمَّ أَتْبَعَ سَبَبا ً
Ĥattá 'Idhā Balagha Maţli`a Ash-Shamsi Wajadahā Taţlu`u `Alá Qawmin Lam Naj`al Lahum Min Dūnihā Sitrāan َ018-090 Har a lõkacin da ya isa ga mafitar rãnã, ya sãme ta tanã fita a kan waɗansu mutãne (waɗanda) ba Mu sanya musu wata kãriya ba daga barinta. حَتَّى إِذَا بَلَغَ مَطْلِعَ الشَّمْسِ وَجَدَهَا تَطْلُعُ عَلَى قَوْم ٍ لَمْ نَجْعَلْ لَهُمْ مِنْ دُونِهَا سِتْرا ً
Kadhālika Wa Qad 'Aĥaţnā Bimā Ladayhi Khuban َ018-091 Kamar wancan alhãli kuwa haƙĩƙa, Mun kẽwaye da jarrabãwa ga abin da ke gunsa. كَذَلِكَ وَقَدْ أَحَطْنَا بِمَا لَدَيْهِ خُبْرا ً
Thumma 'Atba`a Sababāan َ018-092 Sa'an nan kuma ya bi hanya. ثُمَّ أَتْبَعَ سَبَبا ً
Ĥattá 'Idhā Balagha Bayna As-Saddayni Wajada Min Dūnihimā Qawmāan Lā Yakādūna Yafqahūna Qawlāan َ018-093 Har a lõkacin da ya isa a tsakãnin duwãtsu biyu, ya sãmi waɗansu mutãne daga gabãninsu. Ba su yi kusa su fahimci magana ba. حَتَّى إِذَا بَلَغَ بَيْنَ السَّدَّيْنِ وَجَدَ مِنْ دُونِهِمَا قَوْما ً لاَ يَكَادُونَ يَفْقَهُونَ قَوْلا ً
Qālū Yā Dhā Al-Qarnayni 'Inna Ya'jūja Wa Ma'jūja Mufsidūna Fī Al-'Arđi Fahal Naj`alu Laka Kharjāan `Alá 'An Taj`ala Baynanā Wa Baynahum Saddāan َ018-094 Suka ce: "Yã Zulƙarnaini! Lalle ne Yãjũja da Majũja mãsu ɓarna ne a cikin ƙasa. To, ko zã mu Sanya harãji sabõda kai, a kan ka sanya wani danni a tsakãninmu da tsakãninsu?" قَالُوا يَاذَا الْقَرْنَيْنِ إِنَّ يَأْجُوجَ وَمَأْجُوجَ مُفْسِدُونَ فِي الأَرْضِ فَهَلْ نَجْعَلُ لَكَ خَرْجاً عَلَى أَنْ تَجْعَلَ بَيْنَنَا وَبَيْنَهُمْ سَدّا ً
Qāla Mā Makkananī Fīhi Rabbī Khayrun Fa'a`īnūnī Biqūwatin 'Aj`al Baynakum Wa Baynahum Radan َ018-095 Ya ce: "Abin da Ubangijĩna Ya mallaka mini, a cikinsa yã fi zama alhẽri. Sai ku taimakeni da ƙarfi, in sanya babbar katanga a tsakãninku da tsakãninsu." قَالَ مَا مَكَّنَنِي فِيه ِِ رَبِّي خَيْر ٌ فَأَعِينُونِي بِقُوَّةٍ أَجْعَلْ بَيْنَكُمْ وَبَيْنَهُمْ رَدْما ً
'Ātūnī Zubara Al-Ĥadīdi  ۖ  Ĥattá 'Idhā Sāwá Bayna Aş-Şadafayni Qāla Anfukhū  ۖ  Ĥattá 'Idhā Ja`alahu Nārāan Qāla 'Ātūnī 'Ufrigh `Alayhi Qiţan َ018-096 "Ku kãwo mini guntãyen baƙin ƙarfe". (Suka kai masa) har a lõkacin da ya daidaita a tsakãnin duwãtsun biyu (ya sanya wutã a cikin ƙarfen) ya ce: "Ku hũra (da zugãzugai)." Har a lõkacin da ya mayar da shi wutã, ya ce: "Ku kãwo mini gaci (narkakke) in zuba a kansa." آتُونِي زُبَرَ الْحَدِيدِ  ۖ  حَتَّى إِذَا سَاوَى بَيْنَ الصَّدَفَيْنِ قَالَ انفُخُوا  ۖ  حَتَّى إِذَا جَعَلَه ُُ نَارا ً قَالَ آتُونِي أُفْرِغْ عَلَيْهِ قِطْرا ً
Famā Asţā`ū 'An Yažharūhu Wa Mā Astaţā`ū Lahu Naqan َ018-097 Dõmin haka bã za su iya hawansa ba, kuma bã zã su iya hujẽwa gare shi ba. فَمَا اسْطَاعُوا أَنْ يَظْهَرُوه ُُ وَمَا اسْتَطَاعُوا لَه ُُ نَقْبا ً
Qāla Hādhā Raĥmatun Min Rabbī  ۖ  Fa'idhā Jā'a Wa`du Rabbī Ja`alahu Dakkā'a  ۖ  Wa Kāna Wa`du Rabbī Ĥaqqāan َ018-098 Ya ce: "Wannan wata rahama ce daga Ubangijĩna. Sai idan wa'adin Ubangijĩna ya zo, ya mayar da shi niƙaƙƙe. Kuma wa'adin Ubangijĩna ya kasance tabbatacce." قَالَ هَذَا رَحْمَة ٌ مِنْ رَبِّي  ۖ  فَإِذَا جَاءَ وَعْدُ رَبِّي جَعَلَه ُُ دَكَّاءَ  ۖ  وَكَانَ وَعْدُ رَبِّي حَقّا ً
Wa Taraknā Ba`đahum Yawma'idhin Yamūju Fī Ba`đin  ۖ  Wa Nufikha Fī Aş-Şūri Fajama`nāhum Jaman َ018-099 Kuma Muka bar sãshensu a rãnar nan, yanã garwaya a cikin sãshe, kuma aka bũsa a cikin ƙaho sai muka tãra su, tãrãwa. وَتَرَكْنَا بَعْضَهُمْ يَوْمَئِذ ٍ يَمُوجُ فِي بَعْض ٍ  ۖ  وَنُفِخَ فِي الصُّورِ فَجَمَعْنَاهُمْ جَمْعا ً
Wa `Arađnā Jahannama Yawma'idhin Lilkāfirīna `Arđāan َ018-100 Kuma Muka gitta Jahannama, a rãnar nan ga kãfirai gittãwa. وَعَرَضْنَا جَهَنَّمَ يَوْمَئِذ ٍ لِلْكَافِرِينَ عَرْضا ً
Al-Ladhīna Kānat 'A`yunuhumGhā'in `An Dhikrī Wa Kānū Lā Yastaţī`ūna Saman َ018-101 Waɗanda idãnunsu suka kasance a cikin rufi daga tunã Ni, kuma sun kasance bã su iya saurãrãwa. الَّذِينَ كَانَتْ أَعْيُنُهُمْ فِي غِطَاءٍ عَنْ ذِكْرِي وَكَانُوا لاَ يَسْتَطِيعُونَ سَمْعا ً
'Afaĥasiba Al-Ladhīna Kafarū 'An Yattakhidhū `Ibādī Min Dūnī 'Awliyā'a  ۚ  'Innā 'A`tadnā Jahannama Lilkāfirīna Nuzulāan َ018-102 Shin fa, waɗanda suka kãfirta sun yi zaton (daidai ne) su riƙi waɗansu bãyĩNa, majiɓinta baiciNa? Lalle ne, Mun yi tattalin Jahannama ta zama liyãfa ga kãfirai. أَفَحَسِبَ الَّذِينَ كَفَرُوا أَنْ يَتَّخِذُوا عِبَادِي مِنْ دُونِي أَوْلِيَاءَ  ۚ  إِنَّا أَعْتَدْنَا جَهَنَّمَ لِلْكَافِرِينَ نُزُلا ً
Qul Hal Nunabbi'ukum Bil-'Akhsarīna 'A`mālāan َ018-103 Ka ce: "Kõ mu gaya muku game da mafĩfita hasãra ga ayyuka?" قُلْ هَلْ نُنَبِّئُكُمْ بِالأَخْسَرِينَ أَعْمَالا ً
Al-Ladhīna Đalla Sa`yuhum Al-Ĥayāati Ad-Dunyā Wa Hum Yaĥsabūna 'Annahum Yuĥsinūna Şun`āan َ018-104 "Waɗanda aikinsu ya ɓace a cikin rãyuwar dũniya, alhãli kuwa sunã zaton lalle ne sũ, sunã kyautata, (abin da suke gani) aikin ƙwarai?" الَّذِينَ ضَلَّ سَعْيُهُمْ فِي الْحَيَاةِ الدُّنْيَا وَهُمْ يَحْسَبُونَ أَنَّهُمْ يُحْسِنُونَ صُنْعا ً
'Ūla'ika Al-Ladhīna Kafarū Bi'āyāti Rabbihim Wa Liqā'ihi Faĥabiţat 'A`māluhum Falā Nuqīmu Lahum Yawma Al-Qiyāmati Waznāan َ018-105 Waɗancan ne waɗanda suka kãfirta da ãyõyin Ubangijinsu, da kuma haɗuwa da Shi, sai ayyukansu suka ɓãci. Sabõda haka bã zã Mu tsayar musu da awo ba a Rãnar ¡iyãma. أُولَئِكَ الَّذِينَ كَفَرُوا بِآيَاتِ رَبِّهِمْ وَلِقَائِه ِِ فَحَبِطَتْ أَعْمَالُهُمْ فَلاَ نُقِيمُ لَهُمْ يَوْمَ الْقِيَامَةِ وَزْنا ً
Dhālika Jazā'uuhum Jahannamu Bimā Kafarū Wa Attakhadhū 'Āyātī Wa Rusulī Huzūan َ018-106 Wancan ne sakamakonsu shĩ ne Jahannama, sabõda kãfircinsu, kuma suka riƙi ãyõyiNa da ManzanniNa abin izgili. ذَلِكَ جَزَاؤُهُمْ جَهَنَّمُ بِمَا كَفَرُوا وَاتَّخَذُوا آيَاتِي وَرُسُلِي هُزُوا ً
'Inna Al-Ladhīna 'Āmanū Wa `Amilū Aş-Şāliĥāti Kānat Lahum Jannātu Al-Firdawsi Nuzulāan َ018-107 Lalle ne, waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, Aljannar Firdausi ta kasance ita ce liyãfa a gare su. إِنَّ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ كَانَتْ لَهُمْ جَنَّاتُ الْفِرْدَوْسِ نُزُلا ً
Khālidīna Fīhā Lā Yabghūna `Anhā Ĥiwalāan َ018-108 Suna madawwama a cikinta, bã su nẽman makarkata daga barinta. خَالِدِينَ فِيهَا لاَ يَبْغُونَ عَنْهَا حِوَلا ً
Qul Law Kāna Al-Baĥru Midādāan Likalimāti Rabbī Lanafida Al-Baĥru Qabla 'An Tanfada Kalimātu Rabbī Wa Law Ji'nā Bimithlihi Madadāan َ018-109 Ka ce: "Dã tẽku ta kasance tawada ga (rubũtun)kalmõmin Ubangijina, lalle ne dã tẽkun ta ƙãre a gabãnin kalmõmin Ubangijĩna su ƙãre, kuma kõda mun jẽ da misãlinsa dõmin ƙari." قُلْ لَوْ كَانَ الْبَحْرُ مِدَادا ً لِكَلِمَاتِ رَبِّي لَنَفِدَ الْبَحْرُ قَبْلَ أَنْ تَنفَدَ كَلِمَاتُ رَبِّي وَلَوْ جِئْنَا بِمِثْلِه ِِ مَدَدا ً
Qul 'Innamā 'Anā Basharun Mithlukum Yūĥá 'Ilayya 'Annamā 'Ilahukum 'Ilahun Wāĥidun  ۖ  Faman Kāna Yarjū Liqā'a Rabbihi Falya`mal `Amalāan Şāliĥāan Wa Lā Yushrik Bi`ibādati Rabbihi 'Aĥadāan َ018-110 Ka ce: "Nĩ, mutum ne kawai kamarku, anã yin wahayi zuwa gare ni cewa: Lalle ne, Abin bautawarku, Abin bautawa Guda ne, sabõda haka wanda ya kasance yanã fãtan haɗuwa da Ubangijinsa, to, sai ya yi aiki na ƙwarai. Kuma kada ya haɗa kõwa ga bauta wa Ubangijinsa." قُلْ إِنَّمَا أَنَا بَشَر ٌ مِثْلُكُمْ يُوحَى إِلَيَّ أَنَّمَا إِلَهُكُمْ إِلَه ٌ ٌ وَاحِد ٌ  ۖ  فَمَنْ كَانَ يَرْجُوا لِقَاءَ رَبِّه ِِ فَلْيَعْمَلْ عَمَلا ً صَالِحا ً وَلاَ يُشْرِكْ بِعِبَادَةِ رَبِّهِ~ِ أَحَدا ً
Next Sūrah